Shugaban Ghana John Dramani Mahama, ya bayyana kasar Sin a matsayin abokiyar Afirka ta gaske a ko da yaushe. Yana cewa a karkashin tsarin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da kuma dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka, an gina manyan ababen more rayuwa da dama dake kawo gyare-gyare a kasashen Afirka.
John Mahama ya bayyana haka ne yayin da ya yi hira da wakilin babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG a kwanan nan.
Shugaba Mahama ya kara da cewa, Sin ta taka muhimmiyar rawa kan ci gaban kayayyakin more rayuwa a Afirka. Ya ce a wasu yankuna, kamfanonin Sin sun gina layin dogon da suka hade biranen Ghana kuma sun ba da tallafin kudi ga ayyukan samar da wutar lantarki a yankunan karkara. Da yake godewa goyon bayan Sin ga kasarsa, ya ce kusan kashi 90% na yankunan Ghana sun samu wutar lantarki, wanda hakan ya sa ta shiga cikin kasashen da ke da karfin wutar lantarki mafi girma a Afirka.(Safiyah Ma)














