ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Albishir Na Cin Gajiyar Hannun Jarin Da Aka Zuba A Fannin Kiwo A Nan Kusa

by Abubakar Abba
7 months ago
Gwamnatin

Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa, bisa haɗar da ake ci gaba da yi da kuma zuba jari a fannin kiwon dabbobi a ƙasar nan, nan ba da jimawa za a fara samun sakamako mai kyau.

Wannan na zuwa ne, biyo bayan buɗe sabuwar majalisa ta ƙasa ta bunƙasa fannin kiwon dabbobi (NCLD) da aka gudanar a  Yola, babban birnin Jihar Adamawa.

Idi Mukhtar Maiha, Ministan Ma’aikatar Bunƙasa Fannin Kiwon Dabbobi ya shaida wa tawagar da suka fito daga fannin kiwon dabbobi da kuma sauran masu zaman kansu a fannin cewa, an faro wannan aikin ne a shekarar da ta gabata, wadda aka mayar da hankali, musamman a ɓangaren kasuwanci; domin samun riba a fannin samar da Madarar Shanu da kiwon Kajin gidan gona da sauransu.

ADVERTISEMENT
  • Jihar Zamfara Na Da Rinjaye A Fannin Noma, In Ji Gwamna Lawal A Taron AIF Na Morocco
  • Jihar Kaduna Ta Ƙulla Yarjejeniyar Dala Miliyan 200 Da Ƙasar Sin Don Bunƙasa Noman Zamani

Ya ce, tuni abokan haɗakar suka goyi bayan aikin samar da Madarar Shanu da ƙara ƙarfafa zaman lafiya da kuma rage ƙalubalen sauyin yanayi a ɓangaren kiwon dabbobi a ƙasar.

Ya ƙara da cewa, wannan ɗaukin ga fannin zai taimaka wajen ƙara samar da kuɗaɗen shiga ga waɗanda suke a fannin da ƙara kula da lafiyar dabbobi tare da kuma rage yawan afkuwar rikice-rikice a tsakanin manoma da Fulani Makiyaya a ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Maiha ya ci gaba da cewa, sabuwar majalisar za ta kuma taimaka wajen ƙara ƙarfafa haɗaka da jawo ra’ayin masu zuba hannun jari da kuma ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar.

Shi kuwa a nasa jawabin a wajen taron, Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya sanar da cewa; fannin kiwon dabbobi, ba sabon abu ba ne; don an jima ana yin sa a jihar, musamman domin haɓaka tattalin arziƙin jihar.

Fintiri, wanda Mataimakiyarsa Kaletapwa George Farauta, ta wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa; shekaru da dama jihar ta kasance tana da Ma’aikatar Kiwon Dabbobi.

Gwamnan ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta taimaka wa Adamawa, kan ƙoƙarin da take ci gaba da yi na aikin samar da Rugar Kiwon Dabbobi na zamani.

Shi kuwa a saƙonsa a wajen taron, Farfesa Attahiru Jega, Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara ta Musamman a ɓangaren samar da sauye-sauye a fannin kiwon dabbobi, ya yi fatan aikin zai taimaka wajen ƙara bunƙasa tattalin arziƙin masu kiwon dabbobi da kuma magance rikice-rikicen manoma da Fulani Makiyaya.

Jega, wanda Babbar Sakatariya a Ma’aikatar Kiwon Dabbobi, Chinyere Ijeoma Akujobi, ta wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa; buɗe wannan majalisar ta ƙasa, tamkar buɗe wani sabon babi ne a fannin kiwon dabbobi a ƙasar.

Gwamnatin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Nazarin CGTN: An Bukaci Amurka Ta Sa Japan Ta Janye Kalaman Takala Da Ta Furta

Nazarin CGTN: An Bukaci Amurka Ta Sa Japan Ta Janye Kalaman Takala Da Ta Furta

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.