Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa, bisa haɗar da ake ci gaba da yi da kuma zuba jari a fannin kiwon dabbobi a ƙasar nan, nan ba da jimawa za a fara samun sakamako mai kyau.
Wannan na zuwa ne, biyo bayan buɗe sabuwar majalisa ta ƙasa ta bunƙasa fannin kiwon dabbobi (NCLD) da aka gudanar a Yola, babban birnin Jihar Adamawa.
Idi Mukhtar Maiha, Ministan Ma’aikatar Bunƙasa Fannin Kiwon Dabbobi ya shaida wa tawagar da suka fito daga fannin kiwon dabbobi da kuma sauran masu zaman kansu a fannin cewa, an faro wannan aikin ne a shekarar da ta gabata, wadda aka mayar da hankali, musamman a ɓangaren kasuwanci; domin samun riba a fannin samar da Madarar Shanu da kiwon Kajin gidan gona da sauransu.
- Jihar Zamfara Na Da Rinjaye A Fannin Noma, In Ji Gwamna Lawal A Taron AIF Na Morocco
- Jihar Kaduna Ta Ƙulla Yarjejeniyar Dala Miliyan 200 Da Ƙasar Sin Don Bunƙasa Noman Zamani
Ya ce, tuni abokan haɗakar suka goyi bayan aikin samar da Madarar Shanu da ƙara ƙarfafa zaman lafiya da kuma rage ƙalubalen sauyin yanayi a ɓangaren kiwon dabbobi a ƙasar.
Ya ƙara da cewa, wannan ɗaukin ga fannin zai taimaka wajen ƙara samar da kuɗaɗen shiga ga waɗanda suke a fannin da ƙara kula da lafiyar dabbobi tare da kuma rage yawan afkuwar rikice-rikice a tsakanin manoma da Fulani Makiyaya a ƙasar.
Maiha ya ci gaba da cewa, sabuwar majalisar za ta kuma taimaka wajen ƙara ƙarfafa haɗaka da jawo ra’ayin masu zuba hannun jari da kuma ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar.
Shi kuwa a nasa jawabin a wajen taron, Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya sanar da cewa; fannin kiwon dabbobi, ba sabon abu ba ne; don an jima ana yin sa a jihar, musamman domin haɓaka tattalin arziƙin jihar.
Fintiri, wanda Mataimakiyarsa Kaletapwa George Farauta, ta wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa; shekaru da dama jihar ta kasance tana da Ma’aikatar Kiwon Dabbobi.
Gwamnan ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta taimaka wa Adamawa, kan ƙoƙarin da take ci gaba da yi na aikin samar da Rugar Kiwon Dabbobi na zamani.
Shi kuwa a saƙonsa a wajen taron, Farfesa Attahiru Jega, Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara ta Musamman a ɓangaren samar da sauye-sauye a fannin kiwon dabbobi, ya yi fatan aikin zai taimaka wajen ƙara bunƙasa tattalin arziƙin masu kiwon dabbobi da kuma magance rikice-rikicen manoma da Fulani Makiyaya.
Jega, wanda Babbar Sakatariya a Ma’aikatar Kiwon Dabbobi, Chinyere Ijeoma Akujobi, ta wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa; buɗe wannan majalisar ta ƙasa, tamkar buɗe wani sabon babi ne a fannin kiwon dabbobi a ƙasar.














