ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Albishir Na Cin Gajiyar Hannun Jarin Da Aka Zuba A Fannin Kiwo A Nan Kusa

by Abubakar Abba
7 months ago
Gwamnatin

Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa, bisa haɗar da ake ci gaba da yi da kuma zuba jari a fannin kiwon dabbobi a ƙasar nan, nan ba da jimawa za a fara samun sakamako mai kyau.

Wannan na zuwa ne, biyo bayan buɗe sabuwar majalisa ta ƙasa ta bunƙasa fannin kiwon dabbobi (NCLD) da aka gudanar a  Yola, babban birnin Jihar Adamawa.

Idi Mukhtar Maiha, Ministan Ma’aikatar Bunƙasa Fannin Kiwon Dabbobi ya shaida wa tawagar da suka fito daga fannin kiwon dabbobi da kuma sauran masu zaman kansu a fannin cewa, an faro wannan aikin ne a shekarar da ta gabata, wadda aka mayar da hankali, musamman a ɓangaren kasuwanci; domin samun riba a fannin samar da Madarar Shanu da kiwon Kajin gidan gona da sauransu.

ADVERTISEMENT
  • Jihar Zamfara Na Da Rinjaye A Fannin Noma, In Ji Gwamna Lawal A Taron AIF Na Morocco
  • Jihar Kaduna Ta Ƙulla Yarjejeniyar Dala Miliyan 200 Da Ƙasar Sin Don Bunƙasa Noman Zamani

Ya ce, tuni abokan haɗakar suka goyi bayan aikin samar da Madarar Shanu da ƙara ƙarfafa zaman lafiya da kuma rage ƙalubalen sauyin yanayi a ɓangaren kiwon dabbobi a ƙasar.

Ya ƙara da cewa, wannan ɗaukin ga fannin zai taimaka wajen ƙara samar da kuɗaɗen shiga ga waɗanda suke a fannin da ƙara kula da lafiyar dabbobi tare da kuma rage yawan afkuwar rikice-rikice a tsakanin manoma da Fulani Makiyaya a ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Maiha ya ci gaba da cewa, sabuwar majalisar za ta kuma taimaka wajen ƙara ƙarfafa haɗaka da jawo ra’ayin masu zuba hannun jari da kuma ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar.

Shi kuwa a nasa jawabin a wajen taron, Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya sanar da cewa; fannin kiwon dabbobi, ba sabon abu ba ne; don an jima ana yin sa a jihar, musamman domin haɓaka tattalin arziƙin jihar.

Fintiri, wanda Mataimakiyarsa Kaletapwa George Farauta, ta wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa; shekaru da dama jihar ta kasance tana da Ma’aikatar Kiwon Dabbobi.

Gwamnan ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta taimaka wa Adamawa, kan ƙoƙarin da take ci gaba da yi na aikin samar da Rugar Kiwon Dabbobi na zamani.

Shi kuwa a saƙonsa a wajen taron, Farfesa Attahiru Jega, Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara ta Musamman a ɓangaren samar da sauye-sauye a fannin kiwon dabbobi, ya yi fatan aikin zai taimaka wajen ƙara bunƙasa tattalin arziƙin masu kiwon dabbobi da kuma magance rikice-rikicen manoma da Fulani Makiyaya.

Jega, wanda Babbar Sakatariya a Ma’aikatar Kiwon Dabbobi, Chinyere Ijeoma Akujobi, ta wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa; buɗe wannan majalisar ta ƙasa, tamkar buɗe wani sabon babi ne a fannin kiwon dabbobi a ƙasar.

Gwamnatin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Nazarin CGTN: An Bukaci Amurka Ta Sa Japan Ta Janye Kalaman Takala Da Ta Furta

Nazarin CGTN: An Bukaci Amurka Ta Sa Japan Ta Janye Kalaman Takala Da Ta Furta

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.