ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Albishir Na Cin Gajiyar Hannun Jarin Da Aka Zuba A Fannin Kiwo A Nan Kusa

by Abubakar Abba
6 months ago
Gwamnatin

Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa, bisa haɗar da ake ci gaba da yi da kuma zuba jari a fannin kiwon dabbobi a ƙasar nan, nan ba da jimawa za a fara samun sakamako mai kyau.

Wannan na zuwa ne, biyo bayan buɗe sabuwar majalisa ta ƙasa ta bunƙasa fannin kiwon dabbobi (NCLD) da aka gudanar a  Yola, babban birnin Jihar Adamawa.

Idi Mukhtar Maiha, Ministan Ma’aikatar Bunƙasa Fannin Kiwon Dabbobi ya shaida wa tawagar da suka fito daga fannin kiwon dabbobi da kuma sauran masu zaman kansu a fannin cewa, an faro wannan aikin ne a shekarar da ta gabata, wadda aka mayar da hankali, musamman a ɓangaren kasuwanci; domin samun riba a fannin samar da Madarar Shanu da kiwon Kajin gidan gona da sauransu.

ADVERTISEMENT
  • Jihar Zamfara Na Da Rinjaye A Fannin Noma, In Ji Gwamna Lawal A Taron AIF Na Morocco
  • Jihar Kaduna Ta Ƙulla Yarjejeniyar Dala Miliyan 200 Da Ƙasar Sin Don Bunƙasa Noman Zamani

Ya ce, tuni abokan haɗakar suka goyi bayan aikin samar da Madarar Shanu da ƙara ƙarfafa zaman lafiya da kuma rage ƙalubalen sauyin yanayi a ɓangaren kiwon dabbobi a ƙasar.

Ya ƙara da cewa, wannan ɗaukin ga fannin zai taimaka wajen ƙara samar da kuɗaɗen shiga ga waɗanda suke a fannin da ƙara kula da lafiyar dabbobi tare da kuma rage yawan afkuwar rikice-rikice a tsakanin manoma da Fulani Makiyaya a ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Maiha ya ci gaba da cewa, sabuwar majalisar za ta kuma taimaka wajen ƙara ƙarfafa haɗaka da jawo ra’ayin masu zuba hannun jari da kuma ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar.

Shi kuwa a nasa jawabin a wajen taron, Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya sanar da cewa; fannin kiwon dabbobi, ba sabon abu ba ne; don an jima ana yin sa a jihar, musamman domin haɓaka tattalin arziƙin jihar.

Fintiri, wanda Mataimakiyarsa Kaletapwa George Farauta, ta wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa; shekaru da dama jihar ta kasance tana da Ma’aikatar Kiwon Dabbobi.

Gwamnan ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta taimaka wa Adamawa, kan ƙoƙarin da take ci gaba da yi na aikin samar da Rugar Kiwon Dabbobi na zamani.

Shi kuwa a saƙonsa a wajen taron, Farfesa Attahiru Jega, Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara ta Musamman a ɓangaren samar da sauye-sauye a fannin kiwon dabbobi, ya yi fatan aikin zai taimaka wajen ƙara bunƙasa tattalin arziƙin masu kiwon dabbobi da kuma magance rikice-rikicen manoma da Fulani Makiyaya.

Jega, wanda Babbar Sakatariya a Ma’aikatar Kiwon Dabbobi, Chinyere Ijeoma Akujobi, ta wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa; buɗe wannan majalisar ta ƙasa, tamkar buɗe wani sabon babi ne a fannin kiwon dabbobi a ƙasar.

Gwamnatin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Nazarin CGTN: An Bukaci Amurka Ta Sa Japan Ta Janye Kalaman Takala Da Ta Furta

Nazarin CGTN: An Bukaci Amurka Ta Sa Japan Ta Janye Kalaman Takala Da Ta Furta

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.