A yau Asabar, shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Cape Verde Jose Maria Neves, suka tura wa juna sakonni na taya murnar cikar shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashensu.Cikin sakonsa, shugaba Xi na kasar Sin, ya ce cikin shekaru 50 da suka wuce, kasashen Sin da Cape Verde sun nuna yanayi na fahimtar juna, da kokarin rufawa junansu baya a sha’anonin da suka shafi babbar moriyarsu.
Kana kasashen sun aiwatar da hadin gwiwa a fannoni masu alaka da ci gaban tattalin arziki da rayuwar al’umma, inda suka samar da misalin yadda wata babbar kasa da wata karamar kasa suke girmama juna, da kokarin hadin kai a tsakaninsu.
A nasa bangare, shugaba Neves na kasar Cape Verde, ya ce yana godiya ga kasar Sin bisa gudunmowar da ta bayar, ta fuskar tabbatar da ci gaban tattalin arziki mai dorewa a kasar ta Cape Verde.
Kana ana son zurfafa hadin gwiwa tare da kasar Sin, don haifar wa al’ummun kasashen 2 da karin alfanu, in ji shugaba Neves.
Ban da haka, duk dai a yau Asabar, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi musayar sako da takwaransa na kasar Laos, Thongloun Sisoulith, don taya juna murnar cika shekaru 65 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen Sin da Laos. (Bello Wang)















Discussion about this post