Jam’iyyun adawa a Nijeriya sun amince da tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda domin zaɓen 2027, kamar yadda Kabiru Tanimu Turaki, shugaban ɓangare na jam’iyyar PDP, ya bayyana a ranar Asabar.
Turaki ya bayyana hakan ne a taron ƙolin jam’iyyun adawa na ƙasa da aka gudanar a Ibadan, inda shugabannin jam’iyyun siyasa daban-daban suka hallarta domin tsara dabarun siyasa gabanin zaɓen 2027.
Ya ce wannan matsaya na daga cikin ƙoƙarin ƙarfafa haɗin kan jam’iyyun adawa domin ƙara samun damar cin zaɓe, musamman a daidai lokacin da ya ce jam’iyyar APC ke ƙoƙarin tabbatar da cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya zama ɗan takara ba tare da ƙalubale ba a 2027.
A cewarsa: “Duk da matsin lamba da dabarun da APC ke yi domin ganin Shugaba Tinubu ya zama ɗan takara shi kaɗai a 2027, mu za mu tsayar da ‘yan takara kuma mu fafata a zaɓen shugaban ƙasa da sauran zaɓe.”
Ya ƙara da cewa jam’iyyun adawa sun yanke shawarar haɗa kai a kan ɗan takara guda.
“Mun amince cewa za mu yi aiki domin tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda a 2027, wanda dukkan jam’iyyun adawa za su mara masa baya domin ceto ƙasa da jama’arta,” in ji shi.
Taron ya kuma fitar da buƙatar a yi wa shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Joash Ojo Amupitan, murabus kan zargin nuna son kai ga jam’iyyar APC.
A cewar shugabannin adawar, ci gaba da kasancewar Amupitan a kan muƙaminsa na iya rage amincewar jama’a da tsarin zaɓe tare da ƙara zafafa rikicin siyasa gabanin 2027.
Sun ce: “Shugaban INEC, Farfesa Joash Ojo Amupitan, ya nuna son kai ga APC, bai kamata ya jagoranci zaɓen 2027 ba, domin jama’a sun rasa amincewa da shi wajen gudanar da zaɓe cikin gaskiya da adalci.”
Taron ya samu halartar fitattun ‘yan siyasa na adawa ciki har da tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark, da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, inda aka tattauna kan haɗin kai, gyaran tsarin zaɓe, da kuma matsalolin tattalin arziki da tsaro da ake fuskanta a ƙasar.















Discussion about this post