ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyun Adawa A Nijeriya Sun Amince Da Tsayar Da Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Guda A 2027 — Turaki

by Muhammad
1 month ago

Jam’iyyun adawa a Nijeriya sun amince da tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda domin zaɓen 2027, kamar yadda Kabiru Tanimu Turaki, shugaban ɓangare na jam’iyyar PDP, ya bayyana a ranar Asabar.

Turaki ya bayyana hakan ne a taron ƙolin jam’iyyun adawa na ƙasa da aka gudanar a Ibadan, inda shugabannin jam’iyyun siyasa daban-daban suka hallarta domin tsara dabarun siyasa gabanin zaɓen 2027.

Ya ce wannan matsaya na daga cikin ƙoƙarin ƙarfafa haɗin kan jam’iyyun adawa domin ƙara samun damar cin zaɓe, musamman a daidai lokacin da ya ce jam’iyyar APC ke ƙoƙarin tabbatar da cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya zama ɗan takara ba tare da ƙalubale ba a 2027.

ADVERTISEMENT

A cewarsa: “Duk da matsin lamba da dabarun da APC ke yi domin ganin Shugaba Tinubu ya zama ɗan takara shi kaɗai a 2027, mu za mu tsayar da ‘yan takara kuma mu fafata a zaɓen shugaban ƙasa da sauran zaɓe.”

Ya ƙara da cewa jam’iyyun adawa sun yanke shawarar haɗa kai a kan ɗan takara guda.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

“Mun amince cewa za mu yi aiki domin tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda a 2027, wanda dukkan jam’iyyun adawa za su mara masa baya domin ceto ƙasa da jama’arta,” in ji shi.

Taron ya kuma fitar da buƙatar a yi wa shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Joash Ojo Amupitan, murabus kan zargin nuna son kai ga jam’iyyar APC.

A cewar shugabannin adawar, ci gaba da kasancewar Amupitan a kan muƙaminsa na iya rage amincewar jama’a da tsarin zaɓe tare da ƙara zafafa rikicin siyasa gabanin 2027.

Sun ce: “Shugaban INEC, Farfesa Joash Ojo Amupitan, ya nuna son kai ga APC, bai kamata ya jagoranci zaɓen 2027 ba, domin jama’a sun rasa amincewa da shi wajen gudanar da zaɓe cikin gaskiya da adalci.”

Taron ya samu halartar fitattun ‘yan siyasa na adawa ciki har da tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark, da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, inda aka tattauna kan haɗin kai, gyaran tsarin zaɓe, da kuma matsalolin tattalin arziki da tsaro da ake fuskanta a ƙasar.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.