ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyun Adawa A Nijeriya Sun Amince Da Tsayar Da Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Guda A 2027 — Turaki

by Muhammad
3 months ago

Jam’iyyun adawa a Nijeriya sun amince da tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda domin zaɓen 2027, kamar yadda Kabiru Tanimu Turaki, shugaban ɓangare na jam’iyyar PDP, ya bayyana a ranar Asabar.

Turaki ya bayyana hakan ne a taron ƙolin jam’iyyun adawa na ƙasa da aka gudanar a Ibadan, inda shugabannin jam’iyyun siyasa daban-daban suka hallarta domin tsara dabarun siyasa gabanin zaɓen 2027.

Ya ce wannan matsaya na daga cikin ƙoƙarin ƙarfafa haɗin kan jam’iyyun adawa domin ƙara samun damar cin zaɓe, musamman a daidai lokacin da ya ce jam’iyyar APC ke ƙoƙarin tabbatar da cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya zama ɗan takara ba tare da ƙalubale ba a 2027.

ADVERTISEMENT

A cewarsa: “Duk da matsin lamba da dabarun da APC ke yi domin ganin Shugaba Tinubu ya zama ɗan takara shi kaɗai a 2027, mu za mu tsayar da ‘yan takara kuma mu fafata a zaɓen shugaban ƙasa da sauran zaɓe.”

Ya ƙara da cewa jam’iyyun adawa sun yanke shawarar haɗa kai a kan ɗan takara guda.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Mun amince cewa za mu yi aiki domin tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda a 2027, wanda dukkan jam’iyyun adawa za su mara masa baya domin ceto ƙasa da jama’arta,” in ji shi.

Taron ya kuma fitar da buƙatar a yi wa shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Joash Ojo Amupitan, murabus kan zargin nuna son kai ga jam’iyyar APC.

A cewar shugabannin adawar, ci gaba da kasancewar Amupitan a kan muƙaminsa na iya rage amincewar jama’a da tsarin zaɓe tare da ƙara zafafa rikicin siyasa gabanin 2027.

Sun ce: “Shugaban INEC, Farfesa Joash Ojo Amupitan, ya nuna son kai ga APC, bai kamata ya jagoranci zaɓen 2027 ba, domin jama’a sun rasa amincewa da shi wajen gudanar da zaɓe cikin gaskiya da adalci.”

Taron ya samu halartar fitattun ‘yan siyasa na adawa ciki har da tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark, da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, inda aka tattauna kan haɗin kai, gyaran tsarin zaɓe, da kuma matsalolin tattalin arziki da tsaro da ake fuskanta a ƙasar.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
Manyan Labarai

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Next Post
Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.