ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyun Adawa A Nijeriya Sun Amince Da Tsayar Da Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Guda A 2027 — Turaki

by Muhammad
3 months ago

Jam’iyyun adawa a Nijeriya sun amince da tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda domin zaɓen 2027, kamar yadda Kabiru Tanimu Turaki, shugaban ɓangare na jam’iyyar PDP, ya bayyana a ranar Asabar.

Turaki ya bayyana hakan ne a taron ƙolin jam’iyyun adawa na ƙasa da aka gudanar a Ibadan, inda shugabannin jam’iyyun siyasa daban-daban suka hallarta domin tsara dabarun siyasa gabanin zaɓen 2027.

Ya ce wannan matsaya na daga cikin ƙoƙarin ƙarfafa haɗin kan jam’iyyun adawa domin ƙara samun damar cin zaɓe, musamman a daidai lokacin da ya ce jam’iyyar APC ke ƙoƙarin tabbatar da cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya zama ɗan takara ba tare da ƙalubale ba a 2027.

ADVERTISEMENT

A cewarsa: “Duk da matsin lamba da dabarun da APC ke yi domin ganin Shugaba Tinubu ya zama ɗan takara shi kaɗai a 2027, mu za mu tsayar da ‘yan takara kuma mu fafata a zaɓen shugaban ƙasa da sauran zaɓe.”

Ya ƙara da cewa jam’iyyun adawa sun yanke shawarar haɗa kai a kan ɗan takara guda.

LABARAI MASU NASABA

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

“Mun amince cewa za mu yi aiki domin tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda a 2027, wanda dukkan jam’iyyun adawa za su mara masa baya domin ceto ƙasa da jama’arta,” in ji shi.

Taron ya kuma fitar da buƙatar a yi wa shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Joash Ojo Amupitan, murabus kan zargin nuna son kai ga jam’iyyar APC.

A cewar shugabannin adawar, ci gaba da kasancewar Amupitan a kan muƙaminsa na iya rage amincewar jama’a da tsarin zaɓe tare da ƙara zafafa rikicin siyasa gabanin 2027.

Sun ce: “Shugaban INEC, Farfesa Joash Ojo Amupitan, ya nuna son kai ga APC, bai kamata ya jagoranci zaɓen 2027 ba, domin jama’a sun rasa amincewa da shi wajen gudanar da zaɓe cikin gaskiya da adalci.”

Taron ya samu halartar fitattun ‘yan siyasa na adawa ciki har da tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark, da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, inda aka tattauna kan haɗin kai, gyaran tsarin zaɓe, da kuma matsalolin tattalin arziki da tsaro da ake fuskanta a ƙasar.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi

MASU ALAKA

DSS
Manyan Labarai

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026
Manyan Labarai

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
Next Post
Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.