Shugabar ƙungiyar Ƙananan Hukumomin ta Nijeriya (ALGON) a Jihar Kano, Sa’adatu Maijama’a, ta tsallake rijiya da baya bayan da wasu da ake zargin ’yan daba ne, suka kai mata hari a wani taron jam’iyyar APC a garin Rano.
Sa’adatu, wadda ita ce shugabar ƙaramar hukumar Tudun Wada, jami’an tsaron SSS ne suka ceto ta bayan maharan sun nufi inda take suna jifa tare da ƙoƙarin kai mata hari.
Shaidu sun ce lamarin ya faru ne lokacin da take ƙoƙarin shiga wata mota da ke ɗauke da manyan jami’an gwamnati ciki har da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf.
Jami’an SSS sun yi saurin kare ta tare da saka ta cikin motarsu inda suka fice da ita daga wajen.
Wani ganau ya ce maharan sun kuma kai wa motar jami’an tsaron hari yayin da suke ƙoƙarin ceton ta.
Rahotanni sun ce bayan harin, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kira taron gaggawa kan matsalar tsaro da rikice-rikicen daba da ke ƙaruwa a Jihar Kano.
Lamarin na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun yawaitar faɗan daba da faɗace-faɗace da ke da alaƙa da siyasa a wasu sassan jihar.















Discussion about this post