A yau Litinin 12 ga wannan wata, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar cewa, game da ra’ayin Amurka kan halin da Iran ke ciki, kasar Sin ba za ta amince da tsoma baki cikin harkokin cikin gidan sauran kasashe ba, kuma tana kira da a tabbatar da ikon mallakar kasa da tsaron kasa, da kin amincewa da amfani da karfin tuwo yayin da ake daidaita huldar kasa da kasa.
Game da kalaman shugaban kasar Amurka Donald Trump kan tsibirin Greenland, Mao Ning ta bayyana cewa, ya kamata a girmama iko da ‘yancin kasa da kasa kan gudanar da ayyuka a yankin Arctic bisa dokoki. Tana mai cewa bai kamata a maida sauran kasashe dalili ba, yayin da kasar Amurka ke yunkurin neman moriyar kanta.
Game da ra’ayin Amurka kan batun kasar Cuba, Mao Ning ta bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan kasar Cuba wajen tabbatar da ikon mallakar kasa da tsaronta. Ta ce, koda yake an samu sauyi a yanayin duniya, kasar Sin za ta ci gaba da zurfafa hadin gwiwa da kasashen Latin Amurka ciki har da kasar Venezuela don sa kaimi ga samun bunkasuwa tare.
Ban da wannan kuma, game da batun kayyade fitar da kayayyakin amfanin soja da jama’a daga Sin zuwa Japan, Mao Ning ta bayyana cewa, Sin ta dauki matakan ne don tabbatar da tsaro da moriyar kasa, da sauke nauyin dake wuyanta na hana yaduwar makaman nukiliya da sauran ayyukan duniya, tana mai cewa matakin abu ne da ya dace, mai kuma adalci dake bisa doron doka. (Zainab Zhang)















Discussion about this post