Kasashen Japan da Philippines sun ware kasar Sin, inda suka kaddamar da abun da suka kira “tattaunawar iyakance yankunan teku,” wani mataki da ya yi matukar keta hakkoki da muradun Sin na teku, wanda Sin din ta ce ba za ta amince da shi ba.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Lin Jian ne ya bayyana haka yayin taron manema labarai na yau Talata, inda ya nanata cewa, kasar Sin na da yankin tattalin arziki na musamman a cikin teku da ke karkashin cikakken ikonta, kuma akwai bangare na yankinta da ke karkashin ruwan da ke gabas da Tsibirin Taiwan na kasar, yana cewa yunkurin Japan da Philippines ya yi matukar keta dokokin kasa da kasa ciki har da yarjejeniyar MDD kan dokar teku da tushen ka’idojin huldar kasa da kasa.
Har ila yau, a yayin taron na manema labarai na yau, Lin Jian ya amsa tambaya game da matakin Amurka na baya bayan nan, na ayyana wasu kamfanonin fasaha na Sin a matsayin kamfanoni masu alaka da ayyukan soji, inda ya ce Sin na kira ga Amurka ta daina zargin kamfanonin kasarta ba gaira ba dalili, kuma ta gyara kuskurenta. (Fa’iza Mustapha)














Discussion about this post