Majalisar Wakilai ta Tarayya ta gayyaci Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara Kan Tsaro, Nuhu Ribadu, Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa, da takwaransa na harkokin kudi, Taiwo Oyedele, domin yi musu tambayoyi kan karuwar sace mutane a wasu sassan kasar nan.
Musamman, majalisar na son sanin kudaden da aka bai wa Ma’aikatar Tsaro a cikin watanni shida da suka gabata da kuma dalilan da suka sa sakamakon ayyukan tsaro bai kai yadda ake tsammani ba a fadin kasar.
Matsayar majalisar ta biyo bayan amincewa da kudirin gaggawa mai muhimmanci ga jama’a wanda dan majalisar mai wakiltar mazaɓar Gummi/Bukkuyum ta jihar Zamfara, Sulaiman Gumi, ya gabatar a zaman majalisar ranar Talata.
Da yake magana kan kudirin, dan majalisar ya nuna damuwa kan mummunan halin tsaro a Zamfara da sauran sassan yankin Arewa maso Yamma, yana mai cewa sakamakon hare-haren ’yan ta’adda, yankin gaba daya na buƙatar tallafin jin kai da ta kara muni sakamakon mawuyacin halin tattalin arziki.
Ya nuna damuwa cewa ci gaba da zirga-zirgar ’yan bindiga ba tare da wani tsoron jami’an tsaro ba a tsakanin garuruwa, jihohi da maɓoyarsu na kara raunana martabar tsaron kasar, yana mai cewa idan ba a dakatar da wannan hali ba, rayuka da dama za su ci gaba da salwanta tare da durkusar da tattalin arzikin yankin.
Bayan amincewa da kudirin, majalisar ta yanke shawarar gayyatar jami’an gwamnatin a ranar da za a sanar daga baya, tare da buƙatar Ministan Tsaro ya tura isassun jami’an tsaro da kayan aiki na musamman zuwa jihar Zamfara da daukacin yankin Arewa maso Yamma domin karfafa tsaron yankin.














Discussion about this post