Babban sakataren kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin kana shugaban kasar, Xi Jinping, ya ce dangantakar kasarsa da Koriya ta Arewa na kan wani sabon mafari na tarihi, inda suke fuskantar sabbin damammakin ci gaba, kana suna rike da sabbin kudurori masu dacewa da lokutan da ake ciki.
Shugaba Xi, ya bayyana hakan ne a Litinin din nan, cikin wata makala mai dauke da sa hannunsa, wadda aka wallafa a mujallar Rodong Sinmun mallakin gwamnatin Koriya ta Arewa. An wallafa makalar ne gabanin ziyarar aiki da shugaban na Sin zai gudanar a Koriya ta Arewa a yau Litinin zuwa gobe Talata, ziyarar da za ta kasance ta farko cikin shekaru bakwai.
Cikin makalar, shugaba Xi ya ce wanzarwa, da karfafa alakar Sin da Koriya ta Arewa sun zamo tabbatattun manufofi na Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin da gwamnatin Sin, kuma kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da Koriya ta Arewa wajen bunkasa dangantakar sassan biyu ta mahangar manyan tsare-tsare, da dacewar alakarsu da lokutan da ake ciki, da ma burinsu na cimma manyan nasarorin raya dangantakarsu. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post