Gwamnatocin Sin da Zambia sun sanya hannu kan wata yarjejeniyar hadin gwiwa, wadda a karkashin ta Sin za ta samarwa Zambia kudaden tallafi, ta yadda sassan biyu za su yi hadin gwiwar gudanar da wasu ayyuka da suka amince da su.
Da yake jawabi yayin bikin sanya hannu kan yarjejeniyar a birnin Lusaka, fadar mulkin kasar Zambia, jakadan Sin a kasar Han Jing, ya ce yarjejeniyar muhimmiyar shaida ce ta alakar abota dake tsakanin kasashen biyu.
Ya kuma kara da cewa, gwamnatin Sin na aiki tukuru wajen tallafawa kamfanonin Sin, ta yadda za su iya zuba jari a Zambia, domin ingiza bunkasa masana’antun kasar, da zamanantar da su, da kuma fadada ci gaban tattalin arzikin kasar.
A nasa bangare kuwa, ministan kudin kasar Zambia Situmbeko Musokotwane, godiya ya yi ga gwamnatin Sin bisa tallafin, yana mai cewa, sanya hannu kan yarjejeniyar ya biyo bayan nasarar shawarwari da shugabannin kasashen biyu suka cimma. (Mai fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post