Yanzu haka ana shirye-shiryen gudanar da taron koli karo na 16, na wakilan kasashe membobin BRICS masu kula da harkokin tsaron kasa a birnin New Delhi na kasar Indiya, a ranakun 22 da 23 ga watan nan na Yuni.
A cewar kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, memban hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta Sin, kuma ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, zai halarci taron bisa gayyatar da aka yi masa.
Lin, ya kara da cewa yayin taron, bangaren Sin zai yi musayar ra’ayoyi tare da sauran membobin BRICS, dangane da yanayin kasa da kasa da ake ciki, ciki har da batun tsaro, da manyan batutuwan duniya da na shiyyoyi, kana da batun matakan hadin kai da ake dauka na gama-gari da ma na musamman, domin shawo kan tarin kalubalen tsaro, da kimtsawa ta fuskar siyasa don maraba da taron koli na BRICS da zai gudana a watan Satumba.
Ya ce, Sin na fatan bunkasa tuntuba, da tsare-tsare tare da sauran membobin BRICS yayin taron dake tafe, ta yadda za a kai ga kara kyautata hadin gwiwar siyasa, da tsaro, da bayar da gudunmawar wanzar da zaman lafiya da tsaro a duniya. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post