Mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Sun Lei, ya yi kira ga sassan kasa da kasa da su himmatu wajen ingiza matakan siyasa a kasar Libya.
Sun, wanda ya yi kiran a jiya Alhamis yayin zaman kwamitin tsaron majalisar, ya ce cimma matsaya tsakanin bangarorin Libya, dangane da tsare-tsaren aiwatar da zabe, da dunkule hukumomin gwamnatin kasar waje guda, su ne manyan kudurorin dake rataye a wuyan kwamitin na tsaro, a fannin shawo kan yanayin da kasar ke ciki.Sun Lei, ya kara da cewa Sin na maraba da ci gaban ayyukan tawagar MDD mai aiki a Libya, a fannin ingiza aiwatar da tsarin siyasar kasar.
Daga nan sai ya bukaci manyan sassan siyasar kasar da su nuna aniyar siyasa, su sanya muradun kasar da na al’ummunta na dogon lokaci gaban komai, kana su yi aiki tukuru wajen cimma daidaito da matsaya guda. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post