ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
3 months ago
Arewa

Ƙungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta ayyana dokar ta-baci kan harkokin tsaro, tana mai gargaɗin cewa Nijeriya na fuskantar mummunar matsalar tsaro da ke barazana ga zaman lafiyar ƙasa, ci gaban tattalin arziki da haɗin kan al’umma.

A cikin wata sanarwa da kakakin ƙungiyar, Abubakar Jika Jiddere, ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta nuna matuƙar damuwa kan abin da ta bayyana a matsayin ci gaba da durƙushewar tsarin tsaro a faɗin ƙasar, tana mai cewa miliyoyin ƴan Nijeriya na rayuwa cikin tsoro yayin da ƙungiyoyin masu aikata laifuka ke ci gaba da aikata miyagun ayyukansu ba tare da tsoro ba.

Ƙungiyar ta yi nuni da Sashe na 14(2)(b) na Kundin Tsarin Mulkin 1999, wanda ya tanadi cewa tsaro da walwalar ƴan ƙasa su ne babban nauyin gwamnati, tana mai tambayar dalilin da ya sa ake barin mutane su kare kansu daga masu garkuwa da mutane, ƴan ta’adda, ƴan bindiga, masu tsattsauran ra’ayi da sauran ƙungiyoyin masu aikata laifuka.

ADVERTISEMENT

NEF ta bayyana cewa duk da cewa Nijeriya ta fuskanci ƙalubalen tsaro iri-iri a baya, ciki har da Yaƙin Basasa, rikicin Maitatsine, ta’asar Neja Delta, rikice-rikicen addini, fashi da makami da kuma tada ƙayar baya ta Boko Haram, halin da ake ciki yanzu ya bambanta domin matsalolin tsaro daban-daban suna faruwa lokaci guda a kusan dukkan yankunan ƙasar.

Ƙungiyar ta yi nuni da hare-hare da ayyukan ta’addanci da ke faruwa a Jihohin Zamfara, Katsina, Kaduna, Neja, Filato, Binuwe, Kogi, Kwara, Borno, Oyo, Edo, Enugu da Imo da sauransu. Ta ce ana kai hare-hare kan al’ummomi, ana sace mutane, ana korar manoma daga gonakinsu, sannan matafiya na fuskantar hare-hare a manyan hanyoyi.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

NEF ta kuma nuna damuwa kan yadda satar mutane domin neman kuɗin fansa ta zama wata babbar sana’ar laifi da ke samun ƙarfi sakamakon raunin tsarin doka, iyakoki marasa tsaro, yaɗuwar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma rashin ingantacciyar haɗin kai a fannin tattara bayanan sirri.

“Abubuwan da ke faruwa suna da matuƙar muni,” in ji sanarwar, tana mai cewa manoma na barin gonakinsu, samar da abinci na raguwa, tattalin arzikin karkara na durƙushewa, masu zuba jari na rasa ƙwarin gwiwa, yayin da yara da dama ke rasa damar zuwa makaranta saboda rashin tsaro.

Ƙungiyar ta kuma soki yadda ake mayar da martani ga hare-haren tsaro a wasu yankuna, tana mai cewa ana samun jinkiri wajen kai ɗauki yayin hare-hare kuma masu aikata laifuka ba sa fuskantar hukunci yadda ya kamata.

Har ila yau, NEF ta buƙaci a gudanar da cikakken bincike kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba da sauran nau’o’in anfani da albarkatun ƙasa, waɗanda rahotanni daban-daban suka danganta da matsalolin tsaro a wasu sassan ƙasar.

Domin magance matsalar, ƙungiyar ta buƙaci gwamnati ta ɗauki matakai na musamman, ciki har da sake fasalin tsarin tattara bayanan sirri da ƙarfafa haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro, rushe hanyoyin ayyukan masu garkuwa da mutane da ƴan bindiga, da kuma gurfanar da masu ɗaukar nauyi da masu tallafa wa ƙungiyoyin masu aikata laifuka ba tare da la’akari da matsayinsu ba.

Sauran shawarwarin da ta bayar sun haɗa da gudanar da bincike kan duk ayyukan haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba, ƙarfafa tsaron al’ummomin manoma, makarantu da manyan hanyoyin sufuri, da kuma tabbatar da gaskiya da rikon amana wajen kashe kuɗaɗen tsaro.

NEF ta jaddada cewa matsalar tsaro ba ta yanki ko ƙabila ba ce, illa dai matsala ce ta ƙasa baki ɗaya. Ta yi gargaɗin cewa amincewar jama’a ga gwamnati za ta ci gaba da raguwa idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba.

“Wannan ba batun siyasa ba ne. Ba batun yanki ba ne. Ba batun ƙabila ba ne. Wannan matsalar gaggawa ce ta ƙasa baki ɗaya,” in ji sanarwar.

A ƙarshe, ƙungiyar ta yi kira ga shugabanni a kowane mataki da su daina bayar da alƙawuran baki kawai, su mayar da hankali kan samar da sakamako a aikace, tana mai cewa tarihi zai yi hukunci da su bisa rayukan da suka kare da kuma ƙasar da suka taimaka wajen ceto.

“Lokacin bayar da tabbaci ya wuce. Lokacin nuna sakamako a aikace ya yi,” in ji sanarwar.

Arewa
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Arewa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.