Ƙungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta ayyana dokar ta-baci kan harkokin tsaro, tana mai gargaɗin cewa Nijeriya na fuskantar mummunar matsalar tsaro da ke barazana ga zaman lafiyar ƙasa, ci gaban tattalin arziki da haɗin kan al’umma.
A cikin wata sanarwa da kakakin ƙungiyar, Abubakar Jika Jiddere, ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta nuna matuƙar damuwa kan abin da ta bayyana a matsayin ci gaba da durƙushewar tsarin tsaro a faɗin ƙasar, tana mai cewa miliyoyin ƴan Nijeriya na rayuwa cikin tsoro yayin da ƙungiyoyin masu aikata laifuka ke ci gaba da aikata miyagun ayyukansu ba tare da tsoro ba.
Ƙungiyar ta yi nuni da Sashe na 14(2)(b) na Kundin Tsarin Mulkin 1999, wanda ya tanadi cewa tsaro da walwalar ƴan ƙasa su ne babban nauyin gwamnati, tana mai tambayar dalilin da ya sa ake barin mutane su kare kansu daga masu garkuwa da mutane, ƴan ta’adda, ƴan bindiga, masu tsattsauran ra’ayi da sauran ƙungiyoyin masu aikata laifuka.
NEF ta bayyana cewa duk da cewa Nijeriya ta fuskanci ƙalubalen tsaro iri-iri a baya, ciki har da Yaƙin Basasa, rikicin Maitatsine, ta’asar Neja Delta, rikice-rikicen addini, fashi da makami da kuma tada ƙayar baya ta Boko Haram, halin da ake ciki yanzu ya bambanta domin matsalolin tsaro daban-daban suna faruwa lokaci guda a kusan dukkan yankunan ƙasar.
Ƙungiyar ta yi nuni da hare-hare da ayyukan ta’addanci da ke faruwa a Jihohin Zamfara, Katsina, Kaduna, Neja, Filato, Binuwe, Kogi, Kwara, Borno, Oyo, Edo, Enugu da Imo da sauransu. Ta ce ana kai hare-hare kan al’ummomi, ana sace mutane, ana korar manoma daga gonakinsu, sannan matafiya na fuskantar hare-hare a manyan hanyoyi.
NEF ta kuma nuna damuwa kan yadda satar mutane domin neman kuɗin fansa ta zama wata babbar sana’ar laifi da ke samun ƙarfi sakamakon raunin tsarin doka, iyakoki marasa tsaro, yaɗuwar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma rashin ingantacciyar haɗin kai a fannin tattara bayanan sirri.
“Abubuwan da ke faruwa suna da matuƙar muni,” in ji sanarwar, tana mai cewa manoma na barin gonakinsu, samar da abinci na raguwa, tattalin arzikin karkara na durƙushewa, masu zuba jari na rasa ƙwarin gwiwa, yayin da yara da dama ke rasa damar zuwa makaranta saboda rashin tsaro.
Ƙungiyar ta kuma soki yadda ake mayar da martani ga hare-haren tsaro a wasu yankuna, tana mai cewa ana samun jinkiri wajen kai ɗauki yayin hare-hare kuma masu aikata laifuka ba sa fuskantar hukunci yadda ya kamata.
Har ila yau, NEF ta buƙaci a gudanar da cikakken bincike kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba da sauran nau’o’in anfani da albarkatun ƙasa, waɗanda rahotanni daban-daban suka danganta da matsalolin tsaro a wasu sassan ƙasar.
Domin magance matsalar, ƙungiyar ta buƙaci gwamnati ta ɗauki matakai na musamman, ciki har da sake fasalin tsarin tattara bayanan sirri da ƙarfafa haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro, rushe hanyoyin ayyukan masu garkuwa da mutane da ƴan bindiga, da kuma gurfanar da masu ɗaukar nauyi da masu tallafa wa ƙungiyoyin masu aikata laifuka ba tare da la’akari da matsayinsu ba.
Sauran shawarwarin da ta bayar sun haɗa da gudanar da bincike kan duk ayyukan haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba, ƙarfafa tsaron al’ummomin manoma, makarantu da manyan hanyoyin sufuri, da kuma tabbatar da gaskiya da rikon amana wajen kashe kuɗaɗen tsaro.
NEF ta jaddada cewa matsalar tsaro ba ta yanki ko ƙabila ba ce, illa dai matsala ce ta ƙasa baki ɗaya. Ta yi gargaɗin cewa amincewar jama’a ga gwamnati za ta ci gaba da raguwa idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba.
“Wannan ba batun siyasa ba ne. Ba batun yanki ba ne. Ba batun ƙabila ba ne. Wannan matsalar gaggawa ce ta ƙasa baki ɗaya,” in ji sanarwar.
A ƙarshe, ƙungiyar ta yi kira ga shugabanni a kowane mataki da su daina bayar da alƙawuran baki kawai, su mayar da hankali kan samar da sakamako a aikace, tana mai cewa tarihi zai yi hukunci da su bisa rayukan da suka kare da kuma ƙasar da suka taimaka wajen ceto.
“Lokacin bayar da tabbaci ya wuce. Lokacin nuna sakamako a aikace ya yi,” in ji sanarwar.















Discussion about this post