ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 hours ago
Arewa

Ƙungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta ayyana dokar ta-baci kan harkokin tsaro, tana mai gargaɗin cewa Nijeriya na fuskantar mummunar matsalar tsaro da ke barazana ga zaman lafiyar ƙasa, ci gaban tattalin arziki da haɗin kan al’umma.

A cikin wata sanarwa da kakakin ƙungiyar, Abubakar Jika Jiddere, ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta nuna matuƙar damuwa kan abin da ta bayyana a matsayin ci gaba da durƙushewar tsarin tsaro a faɗin ƙasar, tana mai cewa miliyoyin ƴan Nijeriya na rayuwa cikin tsoro yayin da ƙungiyoyin masu aikata laifuka ke ci gaba da aikata miyagun ayyukansu ba tare da tsoro ba.

Ƙungiyar ta yi nuni da Sashe na 14(2)(b) na Kundin Tsarin Mulkin 1999, wanda ya tanadi cewa tsaro da walwalar ƴan ƙasa su ne babban nauyin gwamnati, tana mai tambayar dalilin da ya sa ake barin mutane su kare kansu daga masu garkuwa da mutane, ƴan ta’adda, ƴan bindiga, masu tsattsauran ra’ayi da sauran ƙungiyoyin masu aikata laifuka.

ADVERTISEMENT

NEF ta bayyana cewa duk da cewa Nijeriya ta fuskanci ƙalubalen tsaro iri-iri a baya, ciki har da Yaƙin Basasa, rikicin Maitatsine, ta’asar Neja Delta, rikice-rikicen addini, fashi da makami da kuma tada ƙayar baya ta Boko Haram, halin da ake ciki yanzu ya bambanta domin matsalolin tsaro daban-daban suna faruwa lokaci guda a kusan dukkan yankunan ƙasar.

Ƙungiyar ta yi nuni da hare-hare da ayyukan ta’addanci da ke faruwa a Jihohin Zamfara, Katsina, Kaduna, Neja, Filato, Binuwe, Kogi, Kwara, Borno, Oyo, Edo, Enugu da Imo da sauransu. Ta ce ana kai hare-hare kan al’ummomi, ana sace mutane, ana korar manoma daga gonakinsu, sannan matafiya na fuskantar hare-hare a manyan hanyoyi.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

NEF ta kuma nuna damuwa kan yadda satar mutane domin neman kuɗin fansa ta zama wata babbar sana’ar laifi da ke samun ƙarfi sakamakon raunin tsarin doka, iyakoki marasa tsaro, yaɗuwar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma rashin ingantacciyar haɗin kai a fannin tattara bayanan sirri.

“Abubuwan da ke faruwa suna da matuƙar muni,” in ji sanarwar, tana mai cewa manoma na barin gonakinsu, samar da abinci na raguwa, tattalin arzikin karkara na durƙushewa, masu zuba jari na rasa ƙwarin gwiwa, yayin da yara da dama ke rasa damar zuwa makaranta saboda rashin tsaro.

Ƙungiyar ta kuma soki yadda ake mayar da martani ga hare-haren tsaro a wasu yankuna, tana mai cewa ana samun jinkiri wajen kai ɗauki yayin hare-hare kuma masu aikata laifuka ba sa fuskantar hukunci yadda ya kamata.

Har ila yau, NEF ta buƙaci a gudanar da cikakken bincike kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba da sauran nau’o’in anfani da albarkatun ƙasa, waɗanda rahotanni daban-daban suka danganta da matsalolin tsaro a wasu sassan ƙasar.

Domin magance matsalar, ƙungiyar ta buƙaci gwamnati ta ɗauki matakai na musamman, ciki har da sake fasalin tsarin tattara bayanan sirri da ƙarfafa haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro, rushe hanyoyin ayyukan masu garkuwa da mutane da ƴan bindiga, da kuma gurfanar da masu ɗaukar nauyi da masu tallafa wa ƙungiyoyin masu aikata laifuka ba tare da la’akari da matsayinsu ba.

Sauran shawarwarin da ta bayar sun haɗa da gudanar da bincike kan duk ayyukan haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba, ƙarfafa tsaron al’ummomin manoma, makarantu da manyan hanyoyin sufuri, da kuma tabbatar da gaskiya da rikon amana wajen kashe kuɗaɗen tsaro.

NEF ta jaddada cewa matsalar tsaro ba ta yanki ko ƙabila ba ce, illa dai matsala ce ta ƙasa baki ɗaya. Ta yi gargaɗin cewa amincewar jama’a ga gwamnati za ta ci gaba da raguwa idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba.

“Wannan ba batun siyasa ba ne. Ba batun yanki ba ne. Ba batun ƙabila ba ne. Wannan matsalar gaggawa ce ta ƙasa baki ɗaya,” in ji sanarwar.

A ƙarshe, ƙungiyar ta yi kira ga shugabanni a kowane mataki da su daina bayar da alƙawuran baki kawai, su mayar da hankali kan samar da sakamako a aikace, tana mai cewa tarihi zai yi hukunci da su bisa rayukan da suka kare da kuma ƙasar da suka taimaka wajen ceto.

“Lokacin bayar da tabbaci ya wuce. Lokacin nuna sakamako a aikace ya yi,” in ji sanarwar.

Arewa
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ‘Ƴan Bindiga Sun Hana Manoman Sakkwato Zuwa Gonakinsu, Sun Ƙaƙaba Sabbin Haraji
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matsalar Tsaro:Kashi 60 Na Masana’antu A Arewa Maso Gabas Sun Durƙushe
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Shekarar Musulunci: Tinubu Ya Yi Kira Da A Nuna Kyakkyawan Kishin Ƙasa
Arewa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS
  • Sulaiman
    Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya
  • Sulaiman
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

June 19, 2026
Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
Labarai

Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

June 19, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
Next Post
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

June 19, 2026
Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

June 19, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta

Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta

June 19, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Ƴan Bindiga Sun Hana Manoman Sakkwato Zuwa Gonakinsu, Sun Ƙaƙaba Sabbin Haraji

June 19, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.