Ma’aikatar albarkatun ruwa ta kasar Sin, ta yi kira ga sassan hukumomi masu ruwa da tsaki, da su kara azamar aiwatar da matakan kandagarkin aukuwar bala’u, yayin da ake tunkarar lokacin da a kan fuskanci ambaliyar ruwa a wasu sassa na kasar.
Alkaluman hasashen saukar ruwan sama da aka fitar a hukumance, sun nuna yadda yankunan arewa maso gabashi, da gabashi, da kudu, da kudu maso yammacin kasar Sin, za su samu saukar ruwa da karin kaso 10 zuwa kaso 20, sama da wanda aka saba samu a watan Yuni, wanda hakan ke nuni ga yiwuwar samun ambaliya a wasu yankuna na tsakiyar kogin Yangtze da kogin Pearl.
Ma’aikatar ta yi gargadin cewa, ambaliyar ruwa na iya haifar da yanayi mai wahala da sarkakiya, don haka ta bukaci da a karfafa tsarin gargadi na gaggawa, da shirin tunkarar ayyukan gaggawa.
Kazalika, ma’aikatar ta sha alwashin aikewa da tawagar ma’aikata, da kwararru zuwa wuraren da ake bukata domin samar da jagoranci na kai tsaye.Bugu da kari, ma’aikatar ta ce wajibi ne manyan madatsun ruwa dake yankunan koguna masu fuskantar babban hadarin tsumbatsa, su zamo cikin shirin dakile ambaliyar da shawo kan ibtila’i, yayin da kuma ake ci gaba da matsa kaimin aiki sintiri, da sanya ido kan muhimman shingayen kare ruwa. (Mai fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post