Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari wani masallaci a ƙauyen Namama da ke ƙaramar hukumar Giwa a jihar Kaduna, inda suka kashe wani yaro mai suna Adamu tare da jikkata wasu masu ibada yayin sallar Magariba.
A cewar wani masani kan harkokin tsaro mai suna Bakatsine, maharan sun afka masallacin ne a lokacin da ake gudanar da sallah yayin da ake ruwan sama mai karfi, inda suka buɗe wuta kan masu ibadar ba tare da nuna bambanci ba.
Harin ya yi sanadin mutuwar yaron tare da jikkata wasu mutane da dama, waɗanda aka garzaya da su asibiti domin samun kulawar likitoci. Bakatsine ya ce ana ci gaba da yi wa waɗanda suka jikkata addu’ar samun sauƙi cikin gaggawa.
Lamarin ya sake tayar da hankula kan matsalar rashin tsaro a wasu sassan jihar Kaduna, yayin da mazauna yankunan karkara ke ci gaba da fuskantar hare-haren ‘yan bindiga duk da matakan tsaro da hukumomi ke dauka.















Discussion about this post