ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Inganta Dunkulewar Duniya Da Kyautata Cinikayyar Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Idan har da gaske ake son a ciyar da duniya gaba, to hadin gwiwar siyasa da tattalin arziki, da hadin gwiwa a fannin kirkire-kirkire da inganta kwararrun masana’antu na kasa da kasa sun zama wajibi don tunkarar hadarin kenkene kasuwanci ta hanyar sanya takunkumi, da gurbacewar muhalli, da rikice-rikicen tattalin arziki, da rugujewar tsarin samar da kayayyaki a duniya. Kana, karfafa amincewa da juna yayin hadin gwiwa don shawo kan wadannan kalubalolin na da matukar muhimmanci.

Domin ba da shawara game da yadda za a tunkari wadannan matsalolin, Firaministan kasar Sin Li Qiang ya halarci taron shekara-shekara na dandalin tattaunawar tattalin arzikin duniya (WEF) na shekarar 2024 da aka gudanar a Davos, ya kuma gabatar da muhimmin jawabi a ranar 16 ga wannan wata, kasancewar kasar Sin a gun taron ya nuna cewa, a shirye take ta ci gaba da taka rawar gani, wajen inganta hadin gwiwar tattalin arzikin kasa da kasa da kuma tunkarar matsalolin duniya.

  • Sin Ta Yaba Da Kokarin Kasashe ‘Yan Ba Ruwanmu Wajen Ciyar Da Zaman Lafiya Gaba A Duniya
  • Yin Gyare-Gyare Da Bude Kofa Dabara Ce Ta Raya Fuzhou

Yunkurin da kasar Sin ta yi kan muhimmancin ra’ayin bangarori daban-daban ya ba da tabbacin cewa gudummawar da take bayarwa na ciyar da bil’adama gaba. A cikin shawarwarin da firaministan ya gabatar, ya yi kira da a daidaita manufofin tattalin arziki, da inganta kwararrun masana’antu na kasa da kasa, da hadin gwiwa a fannin kirkire-kirkire, da hadin gwiwa a fannin raya koren muhalli, da hadin gwiwa tsakanin sassan duniya, yayin da ya jaddada aminci tsakanin shugabannin kasashen duniya.

ADVERTISEMENT

Baya ga zaman lafiya da ci gaban kasar Sin, ba shakka kasashen duniya suna sa ido kan irin gudummawar da kasar Sin ke bayarwa wajen kara tabbatar da dunkulewar tattalin arzikin duniya. Kamar yadda Okonjo-Iweala, babbar darektar hukumar cinikayya ta duniya (WTO) ta ce a gefen taron dandalin tattaunawar tattalin arzikin duniya da aka gudanar a Davos, yayin da take bayyana muhimmiyar rawar da kasar Sin ke takawa wajen habaka cinikayyar duniya da kuma ci gaban tattalin arzikin duniya, “Duk abin da ya faru da kasar Sin yana yin tasiri ga duniya, hakan ya sanya taka rawar ganin tattalin arzikin kasar Sin ya kasance maslahar kowa da kowa.”

La’akari da taken dandalin tattaunawar tattalin arziki na duniya na 2024 wato “karfafa amincewa” wanda ya jaddada sauke nauyi, da bude kofa, da daidaita gibi tsakanin kasashe masu tasowa da masu ci gaba, da daidaito don jaddada amincewa da juna yayin da ake warware matsalolin duniya kamar sauyin yanayi, rikice-rikicen shiyya-shiyya, da ci gaban kirkirarriyar basira wato AI, da ingancin tsarin samar da kayayyaki a duniya da farfado da tattalin arziki duk suna dogaro ne ga kwarin gwiwa da aminci tsakanin kasashe masu tasowa da ma masu ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Dole ne dandalin na WEF ya zama kafa mai samar da sauki ga hada-hadar kasuwanci a duniya da kuma kawar da shingayen cinikayya, da kiyaye tsarin samar da kayayyaki. Kasar Sin za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka kan inganta dunkulewar duniya da manufar dandalin WEF ta cire shingaye daga cinikayyar kasa da kasa. (Muhammed Yahaya)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
An Kammala Bitar Wasan Kwaikwayo Karo Na Biyu Na Shirye-Shiryen Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa Na 2024 

An Kammala Bitar Wasan Kwaikwayo Karo Na Biyu Na Shirye-Shiryen Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa Na 2024 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.