Kakakin ma’aikatar kasuwancin kasar Sin, ya ce ko kadan kasar bata gamsu ba, kuma tana matukar adawa da matakin da kungiyar tarayyar Turai EU ta dauka, na sanya kamfanin Sin cikin jerin takunkumai 20 da ta kakabawa kasar Rasha, duk da cewa Sin din ta sha gabatar da korafi da rashin amincewa da hakan.
Kakakin, wanda ya bayyana hakan a Asabar din nan, ya ce Sin ta sha nanata kakkarfar matsayarta, ta kin amincewa da kakaba takunkuman kashin kai daga bangare guda, ba tare da amincewar kwamitin tsaron MDD ba.
Ta kuma yi matukar watsi da matakin EUn na yanke hukuncin kashin kai, kan kamfanonin Sin da ma daidaikun jama’ar kasar.
Kazalika, jami’in ya ce Sin na kira ga EU, da ta gaggauta cire kamfanonin Sin da jama’ar kasar daga jerin takunkuman, ta kuma martaba kudurorin da shugabannin sassan biyu suka cimma, tare da shawo kan damuwar kasashe membobinta ta hanyar shawarwari da tuntuba.
Daga nan sai ya bayyana aniyar kasar Sin ta aiwatar da dukkanin matakai da suka wajaba na kare halastattun hakkoki da moriyar kamfanoninta, yana mai cewa EUn ce za ta dauki alhakin abun da hakan zai haifar. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post