Ma’aikatar albarkatun kasa ta Sin, ta fitar da wani shirin aiki na shekaru biyar, wanda za a aiwatar a kasa baki daya tsakanin shekarar nan ta 2026 zuwa 2030, da nufin bunkasa matakan kandagarkin aukuwar bala’u masu tushe daga karkashin kasa, shirin da zai mayar da hankali ga karfafa juriyar yanayin muhalli, da kyautata ikon daukar matakai daga tushe.
Kundin bayani kan shirin, wanda ma’aikatar ta fitar a Talatar nan, ya bayyana shirin sauyawa iyalai 50,000 matsuguni daga yankuna masu hadari, da aiwatar da ayyukan injiya a sassa sama da 4,200, wadanda ke da yiwuwar fuskantar bala’u, da kawar da abubuwa masu iya illata jama’a a wurare sama da 6,100.
Har ila yau, shirin ya tanadi bukatar karfafa yin safiyon hadurra, da sanya ido, da fitar da tsarin gargadin gaggawa yayin da ake fuskantar sauyin yanayi, kana ya jaddada bukatar nazartar tsarin aukuwar bala’u, wadanda mamakon ruwan sama, da saurin sauyin yanayin samaniya, da yawaitar sauyin yanayin fari ke haifarwa. (Mai fassara: Saminu Alhassan)














