Kasar Sin ta mika aikin gyara da fadada asibitin Masaka na Rwanda ga hukumomin kasar, yayin wani biki da ya gudana jiya Juma’a a babban birnin Kigali.
Aikin wanda Sin ta bayar da tallafin gudanar da shi, shi ne aikin tallafi mafi girma da gwamnatin Sin ta gudanar a Rwanda, kuma wani muhimmin aiki na inganta rayuwa da ke karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya.
Biyo bayan gyara da fadada asibitin, girmansa ya karu daga murabba’in mita 6,398 zuwa murabba’in mita 56,957, yayin da adadin gadaje ya karu sosai daga 127 zuwa 837. An kuma samu karuwar adadin marasa lafiya da asibitin zai iya karba a kullum zuwa 2,000.
Da yake jawabi yayin bikin, ministan lafiya na kasar Sabin Nsanzimana, ya ce wannan wani gagagrumin ci gaba ne ga kasar da kuma bangaren kiwon lafiya.
Ya ce suna sa ran wannan asibiti zai zama alama ta ingantacciyar kiwon lafiya da za su iya samarwa a Rwanda da nahiyar Afrika. Kuma suna sa ran ci gaba da hada hannu da Sin don ganin hadin gwiwar ta fadada a bangaren kiwon lafiya. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)














