A yau Litinin ne kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya ce Sin na adawa da duk wani labari marar dalili na bata mata suna, ko alakanta ta da aikata wani laifi. Guo ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai na yau da kullum, dangane da zargin da wasu ke yi cewa wai Sin na shirin aikewa kasar Iran makamai.
Jami’in ya kara da cewa, har kullum Sin na nacewa matsayarta ta taka-tsantsan, da yin hangen nesa dangane da fitar da kayayyakin da ake iya amfani da su wajen ayyukan soji zuwa ketare, tana kuma kayyade irin wadannan hada-hada bisa dokokin cikin gidanta, da ka’idoji, da nauyin dake wuyanta na cudanyar kasa da kasa.
Guo, ya kara da cewa tattaunawar da Amurka da Iran suka gudanar a kasar Pakistan, mataki ne na sassauta halin da ake ciki, kuma Sin na fatan dukkanin sassa masu ruwa da tsaki za su yi biyayya ga yarjejeniyar tsagaita wutar, kuma za su rungumi matakan siyasa da hanyoyin diflomasiyya wajen warware takaddamar, ta yadda za a kaucewa kara rura wutar tashin hankali, tare da samar da yanayi da zai kai ga dawo da zaman lafiya da walwala a daukacin yankin Gulf.
Daga nan sai ya bayyana matakin tabbatar da tsaro, daidaito, da warware batun mashigin Hormuz, a matsayin buri na daukacin al’ummun kasa da kasa. Kalaman na Guo, na zuwa ne bayan da gwamnatin Amurka ta ce dakarun sojin ruwan kasar za su fara hana jiragen ruwan Iran shige da fice ta mashigin. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post