Ƙungiyar ‘yan majalisa ta jam’iyyar ADC a Majalisar Wakilai ta nemi a cire Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), Farfesa Joash Amupitan, daga muƙaminsa tare da gurfanar da shi a gaban kotu.
Ƙungiyar ta bayyana damuwa kan nuna son-kai da kuma gazawar Amupitan wajen jagorantar zaɓukan shekarar 2027 cikin gaskiya, adalci da sahihanci, bayan wasu kalamansa da ayyukansa da ake zargin sun nuna son zuciya da nuna wariya.
- Yadda Kanal da Sojoji 7 Suka Mutu A Sabon Harin Boko Haram
- Nasir El-Rufai Ya Tattauna Taron ADC Yayin Zuwansa Kotu
‘Yan majalisar sun cimma wannan matsaya ne bayan taronsu na farko da suka gudanar a ranar Lahadi domin nazarin halin da siyasar ƙasar ke ciki.
Da yake ganawa da manema labarai a ranar Litinin a Abuja, shugaban ƙungiyar ADC a Majalisar Wakilai, Hon. Afam Ogene, ya ce wannan kira ya samo asali ne daga abin da suka gani na rashin daidaito da kuma damuwa kan sahihanci da amincin shugaban INEC.
Ogene ya ce ana zargin cewa Amupitan ya taɓa yin kalaman nuna goyon baya ga wata jam’iyya a wani shafinsa na X, inda aka ce ya nuna goyon baya ga jam’iyyar APC mai mulki. Sannan kuma, shafin ya wallafa wasu bayanai da ke zargin ana kashe Kiristoci a Nijeriya.
Dan majalisar ya bayyana cewa, duk da cewa INEC ta musanta cewa Amupitan ba shi ke da wannan shafin na X ba, amma binciken fasahar zamani (digital forensic) da wasu bincike na yanar gizo daga mabambantan tushe sun nuna cewa shafin nasa ne, kuma lambar wayar da aka yi amfani da ita wajen buɗe shafin tana ɗauke da sunansa.
Ya ce wannan lamari na haifar da manyan damuwa game da gaskiya, sahihanci da amincewa, musamman idan aka yi la’akari da muhimmancin muƙamin da yake riƙe da shi.















Discussion about this post