ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ‘Yan Majalisar ADC Sun Nemi A Cire Shugaban INEC, A Gurfanar Da Shi A Gaban Kotu

by Sulaiman
3 months ago
ADC

Ƙungiyar ‘yan majalisa ta jam’iyyar ADC a Majalisar Wakilai ta nemi a cire Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), Farfesa Joash Amupitan, daga muƙaminsa tare da gurfanar da shi a gaban kotu.

 

Ƙungiyar ta bayyana damuwa kan nuna son-kai da kuma gazawar Amupitan wajen jagorantar zaɓukan shekarar 2027 cikin gaskiya, adalci da sahihanci, bayan wasu kalamansa da ayyukansa da ake zargin sun nuna son zuciya da nuna wariya.

ADVERTISEMENT
  • Yadda Kanal da Sojoji 7 Suka Mutu A Sabon Harin Boko Haram
  • Nasir El-Rufai Ya Tattauna Taron ADC Yayin Zuwansa Kotu

‘Yan majalisar sun cimma wannan matsaya ne bayan taronsu na farko da suka gudanar a ranar Lahadi domin nazarin halin da siyasar ƙasar ke ciki.

 

LABARAI MASU NASABA

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

Da yake ganawa da manema labarai a ranar Litinin a Abuja, shugaban ƙungiyar ADC a Majalisar Wakilai, Hon. Afam Ogene, ya ce wannan kira ya samo asali ne daga abin da suka gani na rashin daidaito da kuma damuwa kan sahihanci da amincin shugaban INEC.

 

Ogene ya ce ana zargin cewa Amupitan ya taɓa yin kalaman nuna goyon baya ga wata jam’iyya a wani shafinsa na X, inda aka ce ya nuna goyon baya ga jam’iyyar APC mai mulki. Sannan kuma, shafin ya wallafa wasu bayanai da ke zargin ana kashe Kiristoci a Nijeriya.

 

Dan majalisar ya bayyana cewa, duk da cewa INEC ta musanta cewa Amupitan ba shi ke da wannan shafin na X ba, amma binciken fasahar zamani (digital forensic) da wasu bincike na yanar gizo daga mabambantan tushe sun nuna cewa shafin nasa ne, kuma lambar wayar da aka yi amfani da ita wajen buɗe shafin tana ɗauke da sunansa.

 

Ya ce wannan lamari na haifar da manyan damuwa game da gaskiya, sahihanci da amincewa, musamman idan aka yi la’akari da muhimmancin muƙamin da yake riƙe da shi.

ADC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki
  • Sulaiman
    Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

MASU ALAKA

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya
Manyan Labarai

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe
Siyasa

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed
Siyasa

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

June 27, 2026
Next Post
Kamfanin Sin Ya Gina Fitacciyar Gada Domin Hada Sassan Yankin Neja-Delta A Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Gina Fitacciyar Gada Domin Hada Sassan Yankin Neja-Delta A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.