Rukuni na uku na kwararrun jami’an lafiya da gwamnatin kasar Sin ta tura janhuriyar dimokaradiyyar Congo, ya isa birnin Kinshasa fadar mulkin kasar a ranar Asabar daya ga watan nan na Agusta.
Da yake tsokaci game da hakan a Talatar nan, lokacin da aka yi masa tambaya game da ci gaban yaduwar cutar Ebola a janhuriyar dimokaradiyyar Congo, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce Sin a shirye take ta ci gaba da samar da tallafi daidai karfinta ga kasashen Afirka.
A daya bangaren kuma, dangane da sanarwar da sashen tsaron kasar Philippine ya fitar, wadda ta anbato dokar hadin kai da ci gaban janhuriyar jama’ar kasar Sin, Lin Jian ya ce sanarwar na cike da karairayi, da yunkurin shafawa Sin bakin fenti, da ma tsoma baki cikin harkokin cikin gidan Sin, wanda hakan mummunar tsokana ce irin ta siyasa. Kuma Sin na matukar adawa da hakan. (Mai fassara: Saminu Alhassan)














