Ma’aikatar kudi ta kasar Sin ta sanar da ware kudi har yuan biliyan 99.9, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 14.65, domin tallafawa ayyukan gwamnatin tsakiya na kula da lafiyar yara a shekarar nan ta 2026.
Adadin da aka ware a bana ya karu da kaso 10.6 bisa dari kan na shekarar 2025, wanda kuma bangare ne na yunkurin tallafawa tsarin kiwon lafiyar yara na kasa.
A cewar ma’aikatar, adadin kudin a bana, idan an hada da na asusun kananan hukumomi zai kai kimanin yuan biliyan 110. Ma’aikatar kudin ta kara da cewa, za ta ci gaba da aiki tare da hukumar kiwon lafiya ta kasar wajen amfani da kudaden yadda ya kamata, da karfafa sanya ido, tare da taimakawa wajen gina al’umma mai samar da gata ga yaran da ake haifa a cikinta. (Mai fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post