Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Fu Cong, ya ce an samu sassauci da sararawar yanayi yanzu haka a Gabas ta Tsakiya, kuma yana fatan dorewar hakan, tare da samar da yanayi mai gamsarwa na warware sauran batutuwan dake damun yankin, cikin har da batun zirin Gaza.
Fu Cong, ya bayyana hakan ne a jiya Alhamis, cikin jawabin da ya gabatar a zaman muhawarar gaggawa ta kwamitin tsaron MDD, dangane da batun Falasdinu da Isra’ila. Ya ce a halin yanzu, fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba dake zirin Gaza, na ci gaba da rasa rayukansu a kullum, kana dakarun Isra’ila na ci gaba da fadada ayyukan soji, da fadada yanki mai tsaro ga ‘yan kasar, yayin da Isra’ilan ke barazanar kwace iko da kaso 70 bisa dari na daukacin zirin Gaza, lamarin da ya yi matukar daga hankalin kasar Sin.
Daga nan sai jami’in ya ce Sin na fatan dukkanin sassa, musamman Isra’ila za su rungumi yarjejeniyar tsagaita wuta, tare da dakatar da duk wasu matakai masu hadari, daka iya illata yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma. A lokaci guda kuma, Sin na kira ga Isra’ila da ta yi biyayya ga daukacin ka’idojin jin kai na kasa da kasa, ta tabbatar da ta bayar da damar shigar da kayayyakin agajin gaggawa da ake bukatar shigarwa Gaza. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post