A yau Juma’a, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya ce Sin ta yi kakkausan martani, game da shawagi da barazana da wani jirgin saman yaki da jiragen ruwa masu nutso a teku na kasar New Zealand ya yi, a yankunan Rawayen Teku da tekun kudancin kasar Sin.
Guo, wanda ya bayyana hakan yayin da yake amsa tambayar da aka yi masa dangane da wannan batu, ya ce tuni Sin ta gabatar da kakkarfan korafi ga New Zealand game da faruwar lamarin.
Ya kuma kara da cewa, kutsen na jirgin yakin New Zealand, ya illata moriyar tsaro ta kasar Sin, ya kuma fadada hadarin aukuwar rashin fahimta da aiwatar da kuskure, kana ya yi karan-tsaye ga tsarin gudanar da harkokin sufurin sama na fararen hula a sassan da lamarin ya wakana.
Jami’in ya kara da cewa, Sin na kira ga New Zealand da ta yi biyayya ga dokar kasa da kasa, da tabbatattun ka’idojin cudanyar kasa da kasa, kana ta martaba muradun Sin na kare ‘yancin kai da tsaro, tare da yin aiki tare wajen kawar da hadurra, da wanzar da odar sufurin sama na fararen hula. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post