A yau Laraba, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya jagoranci taron manema labarai na yau da kullum.Yayin da yake ba da amsa kan tambayar da aka yi masa game da matakan da Sin ta dauka kan barkewar annobar cutar Ebola a Afirka, Guo Jiakun ya bayyana cewa, Sin tana mai da hankali kwarai kan barkewar annobar cutar Ebola a Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo da Uganda, kuma za ta ci gaba da tuntubar kasashen da abin ya shafa. Kana za ta yi iyakacin kokarinta tare da hadin gwiwar al’ummar duniya, domin ba da taimako wajen shawo kan annobar da wuri a kasashen Afirka da abun ya shafa bisa ga yadda annobar ke tafiya da kuma bukatun su a fannin.
Da yake mayar da martani kan jawabin da Lai Ching-te ya yi a yau ranar 20 ga Mayu, Guo Jiakun ya bayyana cewa, Taiwan wani bangare ne na kasar Sin da ba za a iya raba shi da ita ba.
Taiwan bai taba zama kasa ba, kuma a nan gaba, ba zai taba zama kasa ba kwata-kwata. Ya ce abin da ake kira “’Yancin kan Taiwan” da zaman lafiya a mashigar tekun Taiwan, tamkar ruwa da wuta ne, ba za su iya kasancewa tare ba. Kana dogaro ga kasashen waje ko kuma makamai domin neman ‘yancin kansa, mafarki ne kawai da ba zai tabbata ba.Da yake amsa tambaya kan sakamakon farko na tattaunawar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Amurka, Guo Jiakun ya bayyana cewa, shugabannin kasashen biyu sun tattauna sosai kan dangantakar kasashensu a fannonin tattalin arziki da cinikayya a yayin ziyarar da shugaba Trump ya yi a kasar Sin. Kuma bangarorin biyu za su bi ra’ayin bai daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma, da hanzarta tabbatar da sakamakon tattaunawar, sannan su hada kai don aiwatar da shi yadda ya kamata, ta yadda za a samar da karin tabbaci da zaman karko ga hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka a nan gaba, da kuma tattalin arzikin kasa da kasa. (Bilkisu Xin)















Discussion about this post