ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
3 weeks ago
Buba

Sanata Shehu Buba Umar, mai wakiltar mazaɓar Sanatan Bauchi ta Kudu kuma mai neman zama ɗan takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar APC, ya sanar da janyewarsa daga zaɓen fidda gwani na gwamna da aka shirya gudanarwa ranar 21 ga Mayu, 2026, inda ya zargi cewa ana tafka maguɗi da take kundin tsarin mulkin jam’iyyar, dokar zaɓe, da kuma ƙa’idojin dimokuraɗiyyar cikin gida.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwar manema labarai da mai ba shi shawara na musamman kan harƙoƙin yaɗa labarai da sadarwa, Kwamared Sabo Muhammad, da ya fitar wa labarai a Bauchi ranar Laraba.

A cewar sanarwar, matakin da Sanata Buba ya ɗauka ya biyo bayan rashin adalci wajen zaɓukan shugabannin jam’iyyar a matakin jiha musamman kan kujerar sakataren jam’iyyar a matakin jihar da kuma sakataren tsare-tsare.Sabo ya bayyana cewa zaɓukan shugabannin jam’iyyar sun kasance cikin ruɗani da kauce wa ƙa’idoji wanda hakan ya sanya jam’iyyar ta ke tafiya a bai-bai.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ƙara da cewa duk da ƙoƙarin da masu ruwa da tsaki suka yi domin sasanta matsalolin cikin lumana, ba a samu wata nasara ba, lamarin da ya haifar da rashin kyakkyawar tsari a cikin jam’iyyar matakin jihar.

Har ila yau, sanarwar ta tuna da umarnin da aka danganta ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, inda ya buƙaci shugabannin jam’iyya su tabbatar da adalci tare da bai wa dukkan ‘yan takara dama yayin zaɓen fidda gwani, tare da gargaɗi kan duk wani abu da zai iya raunana haɗin kan jam’iyya da tsarin dimokuraɗiyya.

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

Sai dai Sanata Buba ya yi zargin cewa yadda aka gudanar da zaɓukan fidda gwani na APC a matakai daban-daban a Jihar Bauchi bai nuna waɗannan ƙa’idoji ba.

Ya ce tsarin ya kasance cike da kura-kurai, rashin gaskiya da kuma rashin ingantattun hanyoyin gudanar da zaɓe.Ya kuma yi zargin cewa ba a ga jami’an zaɓe a wuraren da aka ware domin gudanar da zaɓukan ba, yayin da aka ce an riga an shirya sakamakon kuma aka sanar da su ba tare da gudanar da ingantaccen zaɓe ba.

A cewarsa, wannan lamari ya janyo babban rashin yarda da sahihancin dukkan tsarin zaɓen na fidda ‘yan takara. Inda ya yi zargin cewa wasu tsiraru ke ɗauki-ɗaura maimakon a bar jama’a su zaɓi waɗanda suka dace.

Sanatan ya kuma tayar da tambayoyi dangane da shirye-shiryen gudanar da zaɓen fidda gwani, ciki har da su waye jami’an zaɓen, ina cibiyoyin kaɗa ƙuri’a da tattara sakamako suke, da yadda aka rarraba kayan zaɓe, tambayoyin da ya ce har lokacin da ya janye daga takarar ba a ba su amsa ba.

Bayan tattaunawa mai zurfi da magoya bayansa, abokan siyasa, ‘yan uwa da masu ruwa da tsaki, Sanata Buba ya bayyana cewa bai da wani zaɓi face janyewa daga zaɓen fidda gwani na gwamna a matsayin nuna rashin amincewa da matakan da suke a cikin jam’iyyar.

Ya bayyana matakin a matsayin abin da ya shafi ƙa’ida da akida, yana mai jaddada cewa dole ne tsarin dimokuraɗiyya ya kasance ƙarƙashin doka, adalci da gaskiya, ba wai ƙarƙashin tasirin wasu tsirarun mutane ba.

Sanata Buba ya buƙaci magoya bayansa da masu yi masa fatan alheri su kasance cikin kwanciyar hankali da jajircewa, yana mai nuna ƙwarin gwiwa cewa adalci zai yi nasara a ƙarshe, tare da miƙa al’amarin ga ikon Allah.

Buba
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing
  • Sulaiman
    Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola
Buba
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Fubara Ya Janye Daga Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamnan Ribas A APC

Fubara Ya Janye Daga Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamnan Ribas A APC

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

June 11, 2026
Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

June 11, 2026
An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

June 11, 2026
Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

June 11, 2026
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

June 11, 2026
Shugaban Sin Na Jagorantar Bunkasa Dangantakar Sin Da Koriya Ta Arewa A Sabon Zamani

Shugaban Sin Na Jagorantar Bunkasa Dangantakar Sin Da Koriya Ta Arewa A Sabon Zamani

June 11, 2026
Nijeriya da Habasha Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dawo Da Fursunonin Nijeriya Sama da 100

Nijeriya da Habasha Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dawo Da Fursunonin Nijeriya Sama da 100

June 11, 2026
Za A Kammala Aikin Bututun Iskar Gas Na AKK A Disambar 2024 – NNPC

Na Yi Matuƙar Mamakin Sammaci A Kaina – Mele Kyari

June 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.