ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 months ago
Buba

Sanata Shehu Buba Umar, mai wakiltar mazaɓar Sanatan Bauchi ta Kudu kuma mai neman zama ɗan takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar APC, ya sanar da janyewarsa daga zaɓen fidda gwani na gwamna da aka shirya gudanarwa ranar 21 ga Mayu, 2026, inda ya zargi cewa ana tafka maguɗi da take kundin tsarin mulkin jam’iyyar, dokar zaɓe, da kuma ƙa’idojin dimokuraɗiyyar cikin gida.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwar manema labarai da mai ba shi shawara na musamman kan harƙoƙin yaɗa labarai da sadarwa, Kwamared Sabo Muhammad, da ya fitar wa labarai a Bauchi ranar Laraba.

A cewar sanarwar, matakin da Sanata Buba ya ɗauka ya biyo bayan rashin adalci wajen zaɓukan shugabannin jam’iyyar a matakin jiha musamman kan kujerar sakataren jam’iyyar a matakin jihar da kuma sakataren tsare-tsare.Sabo ya bayyana cewa zaɓukan shugabannin jam’iyyar sun kasance cikin ruɗani da kauce wa ƙa’idoji wanda hakan ya sanya jam’iyyar ta ke tafiya a bai-bai.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ƙara da cewa duk da ƙoƙarin da masu ruwa da tsaki suka yi domin sasanta matsalolin cikin lumana, ba a samu wata nasara ba, lamarin da ya haifar da rashin kyakkyawar tsari a cikin jam’iyyar matakin jihar.

Har ila yau, sanarwar ta tuna da umarnin da aka danganta ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, inda ya buƙaci shugabannin jam’iyya su tabbatar da adalci tare da bai wa dukkan ‘yan takara dama yayin zaɓen fidda gwani, tare da gargaɗi kan duk wani abu da zai iya raunana haɗin kan jam’iyya da tsarin dimokuraɗiyya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Sai dai Sanata Buba ya yi zargin cewa yadda aka gudanar da zaɓukan fidda gwani na APC a matakai daban-daban a Jihar Bauchi bai nuna waɗannan ƙa’idoji ba.

Ya ce tsarin ya kasance cike da kura-kurai, rashin gaskiya da kuma rashin ingantattun hanyoyin gudanar da zaɓe.Ya kuma yi zargin cewa ba a ga jami’an zaɓe a wuraren da aka ware domin gudanar da zaɓukan ba, yayin da aka ce an riga an shirya sakamakon kuma aka sanar da su ba tare da gudanar da ingantaccen zaɓe ba.

A cewarsa, wannan lamari ya janyo babban rashin yarda da sahihancin dukkan tsarin zaɓen na fidda ‘yan takara. Inda ya yi zargin cewa wasu tsiraru ke ɗauki-ɗaura maimakon a bar jama’a su zaɓi waɗanda suka dace.

Sanatan ya kuma tayar da tambayoyi dangane da shirye-shiryen gudanar da zaɓen fidda gwani, ciki har da su waye jami’an zaɓen, ina cibiyoyin kaɗa ƙuri’a da tattara sakamako suke, da yadda aka rarraba kayan zaɓe, tambayoyin da ya ce har lokacin da ya janye daga takarar ba a ba su amsa ba.

Bayan tattaunawa mai zurfi da magoya bayansa, abokan siyasa, ‘yan uwa da masu ruwa da tsaki, Sanata Buba ya bayyana cewa bai da wani zaɓi face janyewa daga zaɓen fidda gwani na gwamna a matsayin nuna rashin amincewa da matakan da suke a cikin jam’iyyar.

Ya bayyana matakin a matsayin abin da ya shafi ƙa’ida da akida, yana mai jaddada cewa dole ne tsarin dimokuraɗiyya ya kasance ƙarƙashin doka, adalci da gaskiya, ba wai ƙarƙashin tasirin wasu tsirarun mutane ba.

Sanata Buba ya buƙaci magoya bayansa da masu yi masa fatan alheri su kasance cikin kwanciyar hankali da jajircewa, yana mai nuna ƙwarin gwiwa cewa adalci zai yi nasara a ƙarshe, tare da miƙa al’amarin ga ikon Allah.

Buba
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin
  • Sulaiman
    Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba
  • Sulaiman
    An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”
  • Sulaiman
    Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar
Buba
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Fubara Ya Janye Daga Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamnan Ribas A APC

Fubara Ya Janye Daga Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamnan Ribas A APC

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026
Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

July 25, 2026
Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

July 25, 2026
Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

July 25, 2026
Kalolin Kitso Na Zamani: Yadda Ake Yin Fulani Style

Muhimmancin Kula Da Gashi Domin Lafiyarsa Da Kyawunsa

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.