ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 month ago
Buba

Sanata Shehu Buba Umar, mai wakiltar mazaɓar Sanatan Bauchi ta Kudu kuma mai neman zama ɗan takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar APC, ya sanar da janyewarsa daga zaɓen fidda gwani na gwamna da aka shirya gudanarwa ranar 21 ga Mayu, 2026, inda ya zargi cewa ana tafka maguɗi da take kundin tsarin mulkin jam’iyyar, dokar zaɓe, da kuma ƙa’idojin dimokuraɗiyyar cikin gida.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwar manema labarai da mai ba shi shawara na musamman kan harƙoƙin yaɗa labarai da sadarwa, Kwamared Sabo Muhammad, da ya fitar wa labarai a Bauchi ranar Laraba.

A cewar sanarwar, matakin da Sanata Buba ya ɗauka ya biyo bayan rashin adalci wajen zaɓukan shugabannin jam’iyyar a matakin jiha musamman kan kujerar sakataren jam’iyyar a matakin jihar da kuma sakataren tsare-tsare.Sabo ya bayyana cewa zaɓukan shugabannin jam’iyyar sun kasance cikin ruɗani da kauce wa ƙa’idoji wanda hakan ya sanya jam’iyyar ta ke tafiya a bai-bai.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ƙara da cewa duk da ƙoƙarin da masu ruwa da tsaki suka yi domin sasanta matsalolin cikin lumana, ba a samu wata nasara ba, lamarin da ya haifar da rashin kyakkyawar tsari a cikin jam’iyyar matakin jihar.

Har ila yau, sanarwar ta tuna da umarnin da aka danganta ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, inda ya buƙaci shugabannin jam’iyya su tabbatar da adalci tare da bai wa dukkan ‘yan takara dama yayin zaɓen fidda gwani, tare da gargaɗi kan duk wani abu da zai iya raunana haɗin kan jam’iyya da tsarin dimokuraɗiyya.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

Sai dai Sanata Buba ya yi zargin cewa yadda aka gudanar da zaɓukan fidda gwani na APC a matakai daban-daban a Jihar Bauchi bai nuna waɗannan ƙa’idoji ba.

Ya ce tsarin ya kasance cike da kura-kurai, rashin gaskiya da kuma rashin ingantattun hanyoyin gudanar da zaɓe.Ya kuma yi zargin cewa ba a ga jami’an zaɓe a wuraren da aka ware domin gudanar da zaɓukan ba, yayin da aka ce an riga an shirya sakamakon kuma aka sanar da su ba tare da gudanar da ingantaccen zaɓe ba.

A cewarsa, wannan lamari ya janyo babban rashin yarda da sahihancin dukkan tsarin zaɓen na fidda ‘yan takara. Inda ya yi zargin cewa wasu tsiraru ke ɗauki-ɗaura maimakon a bar jama’a su zaɓi waɗanda suka dace.

Sanatan ya kuma tayar da tambayoyi dangane da shirye-shiryen gudanar da zaɓen fidda gwani, ciki har da su waye jami’an zaɓen, ina cibiyoyin kaɗa ƙuri’a da tattara sakamako suke, da yadda aka rarraba kayan zaɓe, tambayoyin da ya ce har lokacin da ya janye daga takarar ba a ba su amsa ba.

Bayan tattaunawa mai zurfi da magoya bayansa, abokan siyasa, ‘yan uwa da masu ruwa da tsaki, Sanata Buba ya bayyana cewa bai da wani zaɓi face janyewa daga zaɓen fidda gwani na gwamna a matsayin nuna rashin amincewa da matakan da suke a cikin jam’iyyar.

Ya bayyana matakin a matsayin abin da ya shafi ƙa’ida da akida, yana mai jaddada cewa dole ne tsarin dimokuraɗiyya ya kasance ƙarƙashin doka, adalci da gaskiya, ba wai ƙarƙashin tasirin wasu tsirarun mutane ba.

Sanata Buba ya buƙaci magoya bayansa da masu yi masa fatan alheri su kasance cikin kwanciyar hankali da jajircewa, yana mai nuna ƙwarin gwiwa cewa adalci zai yi nasara a ƙarshe, tare da miƙa al’amarin ga ikon Allah.

Buba
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar
  • Sulaiman
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
  • Sulaiman
    Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
  • Sulaiman
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
Buba
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi
Manyan Labarai

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

July 1, 2026
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Siyasa

Tinubu Ya Shimfiɗa Wa Arewacin Nijeriya Ayyuka Sama Da Kowane Shugaban Ƙasa – Uba Sani

July 1, 2026
Next Post
Fubara Ya Janye Daga Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamnan Ribas A APC

Fubara Ya Janye Daga Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamnan Ribas A APC

LABARAI MASU NASABA

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.