Sanata Shehu Buba Umar, mai wakiltar mazaɓar Sanatan Bauchi ta Kudu kuma mai neman zama ɗan takarar gwamna a ƙarƙashin jam’iyyar APC, ya sanar da janyewarsa daga zaɓen fidda gwani na gwamna da aka shirya gudanarwa ranar 21 ga Mayu, 2026, inda ya zargi cewa ana tafka maguɗi da take kundin tsarin mulkin jam’iyyar, dokar zaɓe, da kuma ƙa’idojin dimokuraɗiyyar cikin gida.
Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwar manema labarai da mai ba shi shawara na musamman kan harƙoƙin yaɗa labarai da sadarwa, Kwamared Sabo Muhammad, da ya fitar wa labarai a Bauchi ranar Laraba.
A cewar sanarwar, matakin da Sanata Buba ya ɗauka ya biyo bayan rashin adalci wajen zaɓukan shugabannin jam’iyyar a matakin jiha musamman kan kujerar sakataren jam’iyyar a matakin jihar da kuma sakataren tsare-tsare.Sabo ya bayyana cewa zaɓukan shugabannin jam’iyyar sun kasance cikin ruɗani da kauce wa ƙa’idoji wanda hakan ya sanya jam’iyyar ta ke tafiya a bai-bai.
Sanarwar ta ƙara da cewa duk da ƙoƙarin da masu ruwa da tsaki suka yi domin sasanta matsalolin cikin lumana, ba a samu wata nasara ba, lamarin da ya haifar da rashin kyakkyawar tsari a cikin jam’iyyar matakin jihar.
Har ila yau, sanarwar ta tuna da umarnin da aka danganta ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, inda ya buƙaci shugabannin jam’iyya su tabbatar da adalci tare da bai wa dukkan ‘yan takara dama yayin zaɓen fidda gwani, tare da gargaɗi kan duk wani abu da zai iya raunana haɗin kan jam’iyya da tsarin dimokuraɗiyya.
Sai dai Sanata Buba ya yi zargin cewa yadda aka gudanar da zaɓukan fidda gwani na APC a matakai daban-daban a Jihar Bauchi bai nuna waɗannan ƙa’idoji ba.
Ya ce tsarin ya kasance cike da kura-kurai, rashin gaskiya da kuma rashin ingantattun hanyoyin gudanar da zaɓe.Ya kuma yi zargin cewa ba a ga jami’an zaɓe a wuraren da aka ware domin gudanar da zaɓukan ba, yayin da aka ce an riga an shirya sakamakon kuma aka sanar da su ba tare da gudanar da ingantaccen zaɓe ba.
A cewarsa, wannan lamari ya janyo babban rashin yarda da sahihancin dukkan tsarin zaɓen na fidda ‘yan takara. Inda ya yi zargin cewa wasu tsiraru ke ɗauki-ɗaura maimakon a bar jama’a su zaɓi waɗanda suka dace.
Sanatan ya kuma tayar da tambayoyi dangane da shirye-shiryen gudanar da zaɓen fidda gwani, ciki har da su waye jami’an zaɓen, ina cibiyoyin kaɗa ƙuri’a da tattara sakamako suke, da yadda aka rarraba kayan zaɓe, tambayoyin da ya ce har lokacin da ya janye daga takarar ba a ba su amsa ba.
Bayan tattaunawa mai zurfi da magoya bayansa, abokan siyasa, ‘yan uwa da masu ruwa da tsaki, Sanata Buba ya bayyana cewa bai da wani zaɓi face janyewa daga zaɓen fidda gwani na gwamna a matsayin nuna rashin amincewa da matakan da suke a cikin jam’iyyar.
Ya bayyana matakin a matsayin abin da ya shafi ƙa’ida da akida, yana mai jaddada cewa dole ne tsarin dimokuraɗiyya ya kasance ƙarƙashin doka, adalci da gaskiya, ba wai ƙarƙashin tasirin wasu tsirarun mutane ba.
Sanata Buba ya buƙaci magoya bayansa da masu yi masa fatan alheri su kasance cikin kwanciyar hankali da jajircewa, yana mai nuna ƙwarin gwiwa cewa adalci zai yi nasara a ƙarshe, tare da miƙa al’amarin ga ikon Allah.















Discussion about this post