Babbar hukumar kwastam ta kasar Sin ta sanar da cewa, kasar za ta ba waken kofin da suka cancanta na kasashe 53 na Afrika da ke da huldar diplomasiyya da ita, damar shiga kasuwar kasar daga ranar 20 ga watan Yulin 2026.
Waken kofi wanda kasashen Afrika da dama ke samarwa, kuma ginshikin tattalin arzikin kasashen da dama, shi ne amfanin gona na biyu daga nahiyar Afrika bayan busasshen borkono, da ya samu damar shiga kasuwar kasar Sin bayan tsallake duk wasu bincike da tantancewa.
Tuni kasashe kamar na Habasha da Burundi suka samu sahalewar shigar da waken kofinsu cikin kasar Sin, yayin da kasashe kamar Mauritius da Angola da Togo da Guinea da Liberia da Sao Tome da Principe suka mika bukatarsu ta neman shigar da waken kofin kasar Sin. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post