Hukumar kula da lafiya ta kasar Sin (NHC) ta ce wata tawagar kwararrun jami’an lafiya za ta tashi da safiyar yau Talata daga birnin Beijing zuwa Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo, domin tallafawa ayyukan takaitawa da dakile yaduwar cutar Ebola a kasar.
A cewar hukumar, gwamnatin kasar Sin ta yanke shawarar tura manyan kwararrun jami’an lafiyar kasar ne bayan a ranar 17 ga watan Mayu, hukumar lafiya ta duniya (WHO) ta ayyana cutar a matsayin mai bukatar kulawar gaggawa daga kasa da kasa.Ta ce kwararrun da ke da gogewa a ayyukan dakile yaduwar annoba, za su yi aiki tare da tawagar jami’an lafiya na Sin da ke Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo, domin karfafa hadin gwiwa da takwarorinsu na kasar da ma na hukumomin yaki da annoba, da nufin taimakawa wajen dakile yaduwar cutar Ebola.
Kamfanin dillancin labarai na Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo watau ACP, ya ruwaito a jiya Litinin ministan lafiya na kasar Roger Kamba na cewa, adadin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar ya kai 343.
Yayin wata hira da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a baya bayan nan, darakta janar na cibiyar kandagarki da dakile yaduwar cututtuka ta Africa CDC Jean Kaseya ya yi gargadin cewa, takaita tafiye-tafiye saboda fargaba da aka ayyana kan kasashen Afrika saboda bullar cutar Ebola na baya bayan nan, ta kawo tsaiko ga tabbatar da an tafiyar da komai a bayyane, tare da katse muhimman ayyukan kiwon lafiya. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post