Ƙungiyar Kiristocin Nijeriya (CAN), ta buƙaci Gwamnatin Tarayya ta ayyana dokar ta-ɓaci kan harkokin tsaro sakamakon karuwar kashe-kashe, sace-sacen mutane da hare-haren ta’addanci da ke ci gaba da faruwa a sassan ƙasar.
An bayyana wannan buƙata ne a wani taron shugabannin majami’u da aka gudanar a Abuja, inda mahalarta taron suka nuna damuwa kan taɓarɓarewar tsaro da kuma yawaitar mutanen da aka tilasta wa barin gidajensu saboda rikice-rikice.
CAN ta ambaci hare-haren da suka faru a jihohin Oyo, Ogun, Borno, Benuwe da Kogi, tare da nuna damuwa kan sace ɗalibai da malamai, hare-haren da ake kai wa manoma da kuma yaɗuwar laifuffuka zuwa wuraren da a baya ake ganin suna da zaune lafiya.
Ƙungiyar ta buƙaci gwamnati ta ƙara ƙarfafa matakan tsaro, inganta tattara bayanan sirri da kuma hanzarta kafa ‘yansandan jihohi.
Haka kuma ta nemi a sako duk waɗanda aka sace ba tare da wani sharaɗi ba, tare da buƙatar jami’an tsaro su ƙara ƙaimi wajen ceto su.
A cikin shawarwarin da ta fitar, CAN ta ayyana kwanaki uku na zaman makokin ƙasa daga ranar 12 zuwa 14 ga watan Yunin 2026.
Ta kuma ware ranar 14 ga watan Yuni a matsayin “Ɓaƙar Rana” domin tunawa da waɗanda suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren tashin hankali da kuma nuna goyon baya ga iyalan da abin ya shafa.
Wannan kira na CAN ya zo ne yayin da ake ci gaba da nuna damuwa kan yawaitar sace ɗalibai a Nijeriya, musamman bayan hare-haren da suka faru a jihohin Oyo da Borno inda aka sace ɗalibai da malamai da dama.















Discussion about this post