Dakarun rundunar ‘Operation HADIN KAI’ sun daƙile wani harin haɗin gwiwa da ‘yan ta’adda suka kai a Kukareta da ke Jihar Yobe a daren Alhamis, inda suka kashe aƙalla ‘yan ta’adda 24 tare da kwato makamai masu yawa.
A wata sanarwa da aka wallafa a shafin Facebook na rundunar sojin Nijeriya a safiyar Alhamis, an bayyana cewa an kai harin ne a tsakar dare na ranar 23 ga Afrilu, 2026, inda aka shafe sa’o’i ana gwabzawa har zuwa misalin ƙarfe 3:00 na daren. Sai dai sojojin Sector 2 na hadin gwiwa (Arewa ta gabas) sun mayar da martani cikin gaggawa da haɗin kai.
Sanarwar, mai ɗauke da sa hannun Jami’in Yaɗa Labarai, Laftanar Kanal Sani Uba, ta ce sojojin sun “yi nasarar daƙile wani ƙaƙƙarfan harin ta’addanci a yankin Kukareta,” inda suka aiwatar da “tsarin farmaki da kariya” wanda ya tilasta maharan ja da baya cikin ruɗani.
A yayin fafatawar, rahotanni sun nuna cewa sojojin sun yi wa maharan mummunar illa, inda aka kashe ‘yan ta’adda 24 zuwa yanzu, yayin da ake ci gaba da sintiri da bincike a yankin da lamarin ya afku.Hukumomin soji sun kuma tabbatar da kwato manyan makamai da alburusai.
Kayayyakin da aka kwato sun haɗa da bindigogi AK-47 guda 18, manyan bindigogin GPMG guda 3, bindigogin PKT masu sarrafa kansu guda 2, bututun RPG guda 3, bututun mortar guda 2, gurneti guda 4, magazin AK-47 guda 18, da kuma alburusai masu yawa na 7.62mm da ake amfani da su a bindigar PKT.















Discussion about this post