Dakarun Rundunar Haɗin Gwiwa ta ‘Operation FANSAN YAMMA’ sun kashe ‘yan ta’adda da dama a wani hari ta sama da aka kai kan wani taron shugabannin ‘yan ta’adda da ake zargi a Jihar Zamfara.
An gudanar da harin ne a ranar 10 ga Mayu, 2026, bayan samun bayanan sirri cewa wasu kwamandojin ‘yan ta’adda suna gudanar da taro a ƙauyen Tumfa da ke ƙaramar hukumar Shinkafi ta jihar.
An bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da Jami’in Yaɗa Labarai na ‘Operation FANSAN YAMMA’, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya fitar a ranar Litinin.
A cewar rundunar sojin, ana zargin ‘yan ta’addan sun taru ne a wani ɓoyayyen wuri da ke wajen ƙauyen, cikin wani yankin da ke cike da bishiyoyi masu yawa domin kar a gano su.
Sanarwar ta ce dakarun Sashe 2 tare da haɗin gwiwar sashen rundunar sama sun kai harin cikin nasara bayan tabbatar da sahihancin bayanan sirrin da suka samu.
“Harin ya yi nasarar lalata wurin da ‘yan ta’addan ke gudanar da taronsu,” in ji sanarwar.
Rahoton tantance barnar da aka yi bayan harin ya nuna cewa an kashe ‘yan ta’adda da dama, yayin da wasu suka tsere daga yankin.
Bayan harin, rundunar sojin ƙasa suka ƙara zafafa sintiri da bincike a yankin domin kamo waɗanda suka tsere tare da tabbatar da nasarar aikin.















Discussion about this post