Tun daga gobe Juma’a daya ga watan Mayu, Sin za ta fara aiwatar da manufar sokewa kasashen Afirka 53 da ke da huldar diplomasiyya da ita haraji gaba daya.
Wani binciken jin ra’ayin jama’a da babban rukunin gidan rediyo da talabijin na kasar Sin sashin CGTN ya gudanar ga masu amfani da yanar gizo a duniya, ya nuna cewa, kashi 87.3% sun yaba da ra’ayin ciniki mai amfani ga juna na Sin.
Suna ganin cewa, yanzu tsarin kasuwancin duniya na fuskantar kalubale, kuma wannan mataki na Sin zai taimaka wajen sassauta matsalolin ci gaba, da rashin adalcin da kasashen Afirka ke fuskanta, tare da kare adalci na kasa da kasa.
A shekara ta 2025, darajar cinikayya tsakanin Sin da Afirka ta kai dala biliyan 348, adadin da ya karu da kashi 17.7% idan aka kwatanta da shekarar da ta gabacin hakan, ya kuma zama mafi girma a tarihi.
Sin ta ci gaba da zama babbar abokiyar cinikin Afirka a tsawon shekaru 16 a jere. Dangane da hakan, kashi 87.4% sun yi imanin cewa manufar soke haraji gaba daya, za ta kara saurin hade kayayyakin Afirka da babbar kasuwar Sin, kuma za ta kawo karin damar ci gaba ga Afirka.
An gudanar da wannan bincike ne ta dandalolin harsunan Turanci, da Sifaniyanci, da Faransanci, da Larabci da harshen Rasha na shafin yanar gizo na CGTN, kuma a cikin sa’o’i 24, masu amfani da intanet 7,665 sun bayyana ra’ayoyinsu. (Amina Xu)















Discussion about this post