Uwargidar shugaban kasa, Oluremi Tinubu, ta kaddamar da shirin rabon tireloli 100 na shinkafa tare da tallafin kudi na naira biliyan 1.2 ga Malaman addini da marasa karfi a jihohi 19 na Arewacin Nijeriya domin hidimar Babbar Sallah.
Shirin Wanda ofishinsa uwargidar shugaban Kasa Oluremi Tinubu da ofishin Mataimaki na musamman ga shugaban Kasa akan harkokin siyasa suka jagoranta ya samu halarcin dubban Malaman addini da kungiyoyi daga jihohi 19 na Arewacin kasar nan da birnin tarayya Abuja Wanda ya guda a dakin taro na gidan gwanatin Kaduna.
Da yake jawabi yayi taron Mataimaki Na musamman ga shugaban kasa kan harkokin siyasa, Ibrahim Kabiru Masari, ya bayyana cewa shirin ya kunshi raba tallafi ga limamai da na’ibansu da malaman Islamiyya da na tsangayu da kungiyoyin nakassu da marayu da sauran marasa galihu a yankin Arewa.

Masari ya kara da cewa an tsara tsarin rabon yadda zai tabbatar da cewa kowa ya amfana cikin adalci, inda kowace jiha za ta samu tirelan shinkafa guda hudu domin rabawa mabukata.A nasa jawabin Shugaban shirye-shiryen shirin bayar da tallafin Aminu Sani Jaji, ya jaddada muhimmancin taimakon juna, yana mai ambato hadisin Manzon Allah (SAW) da ke karfafa rabon abin da mutum ke so wa kansa ga ‘yan uwansa.
Yace uwargidar shugaban Kasa Oluremi Tinubu mai kishin ci gaba Arewa ce inda yace lokaci yayi da al’ummar yankin Arewa zasu sake marawa shugaban Kasa Bola Tinubu domin ganin ya dawo Kato biyu a zaben 227.
Shi ma Sheikh Halliru Maraya wanda yake wakiltar Malaman addini a taron,ya bayyana cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta kawo gagarumin ci gaba a yankin Arewa, wanda ya sa al’ummar yankin ke shirin ci gaba da mara masa baya a zaben 2027.
Ya kara da cewa ‘yan Arewa ne za su taka rawar gani wajen tabbatar da sake tsayawar Tinubu takara, yana mai cewa za su bashi goyon bayan da ya kamata domin dawowarsa mulki a zabe mai zuwa.
A cewarsa, gwamnatin Tinubu ta bai wa yankin Arewa muhimmanci ta hanyar raba mukamai da dama, ciki har da mukamin Ministan tsaro da Ministan Noma da Ministan Kasafi, wadanda duk ‘yan Arewa ne.Haka kuma, ya ce cikin kasa da shekaru uku gwamnatin ta samar da sabbin jami’o’i har guda 23, tare da rage kudin aikin hajji domin saukaka wa al’umma.
Shirin rabon tallafin na daga cikin kokarin gwamnati na rage radadin talauci da tallafa wa al’ummar da ke cikin bukata musamman a yankin Arewa.















Discussion about this post