ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taimakon Afrika? A Dauki Hakikanin Mataki

by CGTN Hausa
2 years ago
Afrika

Kusan babu wata kasar da take hulda da kasashen Afirka da ba ta bayyana niyyar taimaka musu wajen samun ci gaban tattalin arziki ba. Sai dai kyan alkawari cikawa. Ya kamata a dauki hakikanin mataki wajen taimakon kasashen Afirka maimakon maganar baka kawai.

Hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin, ta fuskar aikin gona, wani misali ne mai kyau kan yadda ake daukar hakikanan matakai wajen raya nahiyar Afirka. A wajen taron kara wa juna sani kan hadin gwiwar Afirka da Sin a fannin fasahohin aikin gona, wanda ya gudana a birnin Sanya na kasar Sin a kwanan baya, masana mahalarta taron na kasashen Afirka da na kasar Sin sun ambaci dimbin sakamakon da aka samu a kokarin yin amfani da fasahohin kasar Sin wajen samar da karin amfanin gona a kasashen Afirka. Misali, irin shinkafar musamman da cibiyar nazarin kimiyya da fasaha masu alaka da aikin gona ta kasar Sin ta ba wasu kasashe 9 dake nahiyar Afirka. Bayan an yi gwajin nomanta, an ga yawan shinkafar da aka samu ya karu da fiye da kashi 20%. A nata bangare, cibiyar nazarin fasahohin aikin gona a wurare masu zafin yanayi ta kasar Sin ta yi kokarin yayata wani sabon nau’in rogo a kasashen Afirka, wanda ya sa yawan rogon da a kan girba ya ninka har sau 4. Haka zalika, a cikin shekaru 10 da suka wuce, an yi amfani da cibiyoyin nuna fasahohin aikin gona na zamani guda 24 da kasar Sin ta kafa a kasashen Afirka, wajen yada wasu fitattun fasahohi fiye da 300, ta yadda yawan amfanin gonar da ake samu bisa matsakaicin matsayi ya karu da kashi 30% zuwa 60%, da haifar da alfanu ga magidanta fiye da miliyan 1 na kasashe daban daban dake nahiyar Afirka…

  • Gwamnatin Tarayya Ta Musanta Sauya Sunan Titin Murtala Muhammed A Abuja
  • Tura Yara Kanana Almajirci A Wannan Hali Na Matsin Rayuwa

Ban da samar da karin amfanin gona, fasahohin kasar Sin sun ba da damar bude sabuwar sana’a a kasashen Afirka. Misali, bangaren noman laimar kwado. Da ma a kasar Rwanda, mutane ba su cin laimar kwado. Daga baya an shigar da fasahar noman laimar kwado ta kasar Sin cikin kasar, sa’an nan sannu a hankali, amfanin gonan ya fara samun karbuwa a cikin al’ummar kasar. A halin yanzu, magidanta fiye da 4000 na kasar Rwanda na gudanar da aikin noman laimar kwado, sana’ar da ta samar da guraben aikin yi ga mutane fiye da dubu 30. To, ga shi, laimar kwado ta zama abinci mai gina jiki ga jama’ar kasashen Afirka, har ma ta zame musu wata hanyar samun wadata.

ADVERTISEMENT

Sai dai bayan da aka samu karin amfanin gona, ya kamata a samu hanyar sayar da su. A wannan fanni, gwamnatin kasar Sin ta sanar da bude hanya mai sauki ga shigowar amfanin gonan kasashen Afirka cikin kasuwannin Sin, a watan Nuwamban shekarar 2021, inda aka rage lokacin da ake bukata wajen tantance ingancin kaya, da yafe wa karin kayayyakin kasashen Afirka harajin kwastam, ta yadda aka ba kasashen Afirka damar sayar da dimbin amfanin gonarsu na musamman a kasar Sin. Zuwa yanzu, kasar Sin ta riga ta zama kasa ta biyu a duniya, da aka sayar mata da mafi yawan kayayyakin gonan kasashen Afirka.

Ban da wannan kuma, wani abun da ya fi muhimmanci shi ne, don tabbatar da ci gaba mai dorewa na bangaren aikin gonan kasashen Afirka, ana bukatar samun dimbin matasa ‘yan kasashen Afirka masu kwarewar aiki. A wannan fanni, bisa alkaluman da aka sanar a wajen taron karawa juna sani na wannan karo, cibiyar nazarin kimiyya da fasaha masu alaka da aikin gona ta kasar Sin ta horar da kwararru masu fasahar aikin gona 276 na kasashen Afirka. Kana a nata bangare, jami’ar aikin gona ta Nanjing na kasar Sin ta taimaki kasashen Afirka wajen horar da kwararru masu fasahar noma na matakai daban daban 345, tun daga shekarar 2003…

LABARAI MASU NASABA

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

Ta haka za mu iya ganin cewa, kasar Sin ta dade tana zuba dimbin kudi a kasashen Afirka, da daukar hakikanan matakai a kokarin raya bangaren aikin gona a kasashen, musamman ma a fannonin kyautata fasahohi, da raya sana’o’i, da ingiza bangaren sayayya, gami da horar da kwararru.

Sai dai watakila za ku so ku yi tambaya kan dalilin da ya sa taimakon kasar Sin ga kasashen Afirka cike yake da gaskiya da sahihanci?

Dalili shi ne, domin Sinawa su ma sun taba fama da talauci da yunwa. Kamar yadda tsohon shugaban cibiyar nazarin kimiyya ta nahiyar Afirka, Felix Dakora, wanda shi ma ya halarci taron karawa juna sani na wannan karo, ya fada, kasar Sin ita ma ta taba fuskantar karancin abinci, amma daga bisani ta tabbatar da tsaron abinci, ta hanyar kirkiro sabbin fasahohi a kai a kai, ta yadda take amfani da gonakin da yawansu ya kai kashi 9% na jimillar duniya, wajen samar da abincin da yawansu ya kai kashi 1 cikin kashi 4 na daukacin abincin duniya. Yadda kasar Sin ta samu nasarar raya kanta a lokacin da take fama da koma bayan tattalin arziki, ya sa kasar samun cikakken imani kan cewa, za a iya tabbatar da ci gaban tattalin arziki, ta hanyar hada fasahohin zamani, da ingantattun manufofi, da niyyar aiwatar da manufofi a waje guda, kana mabambantan kasasahe za su iya more ci gaban tattalin arziki tare, gami da samun alfanu na bai daya, yayin da daukacin al’ummar dan Adam ke da damar tabbatar da makomarsu, ta samun ci gaba da wadata na bai daya.

Wani shehun malami na jami’ar Cambridge ta kasar Birtaniya, Ha-Joon Chang, ya bayyana a cikin littafinsa mai taken “tarkon kasashe masu sukuni” da cewa, wasu kasashe masu sukuni sun kwaci dimbin dukiyoyi daga wuraren da suka yi musu mulkin mallaka, don tabbatar da fifikonsu a fannin ci gaban tattalin arziki, daga baya sun yi amfani da dabaru daban daban don neman “cire tsanin da kasashe masu tasowa za su iya amfani da shi wajen hawa sama (Ana nufin samun cikakken ci gaba)”, ta yadda fifikonsu zai dore. To, idan mun iya ci gaba da yin shagube kamar haka, abun da kasar Sin take yi yanzu, shi ne kokarin hadin kai tare da sauran kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka, wajen jingina wani sabon tsani mai inganci a jikin bango, sa’an nan su taka tsanin su hau sama tare, don neman cika burinsu na samun ci gaba na bai daya. (Bello Wang)

Afrika
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

MASU ALAKA

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

July 1, 2026
Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin

June 30, 2026
Next Post
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Yaki Da Ambaliya Da Fari

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Yaki Da Ambaliya Da Fari

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.