Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Sanata Aminu Tambuwal, ya bayyana matukar alhininsa kan harin ’yan bindiga da aka kai wa al’ummar Dangulbi da ke karamar hukumar Tureta a jihar Sokoto.
A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, Tambuwal ya yi Allah-wadai da kashe-kashe, lalata dukiyoyi da kuma raba mazauna yankin da muhallansu da harin ya haifar, yana mai cewa ci gaba da kai hare-hare kan mutanen da ba su ji ba su gani ba, abu ne da ba za a amince da shi ba.
Ya ce, “Na shiga cikin bakin ciki matuka da kuma alhini kan hare-haren da aka kai wa al’ummar Dangulbi. Wadannan hare-hare da ake ci gaba da kai wa kan bayin Allah marasa laifi suna da matukar radadi, ba abin da za a amince da shi ba ne kuma hari ne kai tsaye kan zaman lafiya da tsaron al’ummominmu.”
Sanatan ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu a harin tare da yi wa wadanda suka jikkata addu’ar samun saukin gaggawa. Haka kuma ya jajanta wa mazauna yankin da rikicin ya raba da gidajensu ko ya shafa.














