Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Sanata Aminu Tambuwal, ya bayyana matukar alhininsa kan harin ’yan bindiga da aka kai wa al’ummar Dangulbi da ke karamar hukumar Tureta a jihar Sokoto.
A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, Tambuwal ya yi Allah-wadai da kashe-kashe, lalata dukiyoyi da kuma raba mazauna yankin da muhallansu da harin ya haifar, yana mai cewa ci gaba da kai hare-hare kan mutanen da ba su ji ba su gani ba, abu ne da ba za a amince da shi ba.
Ya ce, “Na shiga cikin bakin ciki matuka da kuma alhini kan hare-haren da aka kai wa al’ummar Dangulbi. Wadannan hare-hare da ake ci gaba da kai wa kan bayin Allah marasa laifi suna da matukar radadi, ba abin da za a amince da shi ba ne kuma hari ne kai tsaye kan zaman lafiya da tsaron al’ummominmu.”
Sanatan ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu a harin tare da yi wa wadanda suka jikkata addu’ar samun saukin gaggawa. Haka kuma ya jajanta wa mazauna yankin da rikicin ya raba da gidajensu ko ya shafa.















Discussion about this post