ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihi Ba Zai Manta Yadda Amurka Ke Zubar Da Jini Da Murƙushe Haƙƙin Ƙasashen Latin Amurka Ba

by Sulaiman
5 months ago
Amurka

Hare-haren da Amurka ta kai wa Venezuela ba wani abu ba ne mai ban mamaki: wannan dai shi ne na kwanan nan a irin al’adarta da ta saba na ayyukan soji domin wargazawa da sauya tsarin gwamnati a duk faɗin Latin Amurka. Daga Guatemala a 1954 zuwa Panama a 1989 da kuma yanzu a Venezuela a 2026, Washington ta yi ta sadaukar da rayuka da ikon gwamnatocin Latin Amurka akai-akai da sunan wai samar da zaman lafiya da kafa dimokuradiyya.

Abin da ya faru a Caracas a 3 ga Janairu abin takaici ne, amma ba abu ne na farko ba, da ma ya riga ya zama al’adar Amurka, gano gwamanti mai fama da ‘yar karamar matsala a cikin gida ko ta shirya manakisar haifar da matsalar, sannan ta fara yi wa kasar barazana, daga nan kuma ta yanke shawarar kashin kanta na amfani da soji wurin sauya gwamnatin.

Amurka ta fara aiwatar da wannan tsarin ne a lokacin da ta hambarar da gwamnatin zababben shugaban Guatemala, Jacobo Arbenz a 1954. Laifinsa ba ta’addanci ko tauye hakkin mutanensa ba ne, kawai ya kawo gyare-gyare ne da za su samar wa kasarsa ‘yancin tattalin arzikinta, ya kalubalanci tsarin tsoma bakin Amurka a harkokin siyasar kasar, wanda hakan zai iya katse abin da Amurka take samu a kasar. Sakon a fili yake, duk kasar da ta nemi ballewa daga bukatun tattalin arzikin Amurka, to gwamnatinta ba za ta tsira ba.

ADVERTISEMENT

Kifar da gwamantin Arbenz da tallafin CIA ya haifar da mika kasar zuwa ga jerin gwamnatocin soji wadanda suka taimaka wajen jefa ƙasar cikin yakin basasa na shekaru 36, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 200,000 galibi ‘yan asalin kasar.

A Chile, matsin lamba na Amurka da kuma kulla manakisa sun taimaka wajen wargaza zababbiyar gwamnatin Salvador Allende sannan kuma sun share fagen juyin mulkin Augusto Pinochet na 1973. Wannan manakisar, ta haifar da mutuwar dubban mutane ko tarwatsa su, sannan ya jefa kasar cikin mummunan yanayin tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

A Nicaragua, lokacin da kungiyar ‘yantar da jama’a ta Sandinista National Liberation Front ta kifar da mulkin kama-karya mai goyon bayan Amurka, Washington ta fara tallafawa sojoji masu adawa da gwamnati a kasar da kudade, ba wai kawai horar da ‘yan adawan ta yi ba, har ma da ƙarfafa su wajen sanya nakiyoyin ruwa a manyan tashoshin jiragen ruwa na kasar. Yakin basasa da Amurka ta haifar ya jefa kasar cikin rikice-rikice, da yawaitar makamai a hannun wadanda ba su cancanta ba na tsawon lokaci. Saboda fama da rikice-rikice na tsawon lokaci, ya mayar da kasar a matsayin daya daga cikin kasashe mafi talauci a Yammacin Duniya.

A Panama, a kokarin Amurka na samun karfin iko na dindindin a mashigin ruwan Panama, ta tura manyan dakarun sojinta a shekarar 1989 don kifar da gwamnatin sojin kasar, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwar kusan ‘yan Panama 500.

Tarihi na nan kuma ba ya tafiya, duk wadannan kasashen da muka ambato muku, Amurka ta yi musu kutse ne da ikirarin samar da ‘yanci, wanzar da zaman lafiya ko kafa dimokuradiyya, amma wacce kasa ce Amurka ta kutsa sannan ta fita ta bar ta da alheri? Sai dai wargazawa, ruguzawa da tarwatsa tattalin arzikin kasar.

Haka in muka duba abin da ya faru kwanan nan a Venezuela, ya yi daidai da irin tsarin da Amurka ta aiwatar a kasashen da muka ambato a baya. Ta tura jiragen sama na yaki masu saukar angulu da dama cikin kasar a tsakar dare, ta kaddamar da hare-hare a Caracas, da kuma kama Shugaban kasa mai ‘yanci, Nicolas Maduro, duk akan wannan ikirarin nata da ta saba, wai samar da zaman lafiya da bayar da tsaro a yankin Latin Amurka. Amma duniya ta san ainihin manufar Amurka.

Abu mafi muni da aka fi tsoro, mummunan tarihin irin abun da ya faru da Guatemala, da Chile, da Nicaragua, zuwa Panama, wanda ya nuna karfin bindigar Amurka baya haifar da dimokuradiyyar da take ikirari face haifar da rikice-rikice da tabarbarewar tattalin arzikin kasa.

Yankin Latin Amurka, ba dajin Allah ba ne zalla da babu mai shi, ballantana Amurka ta ce, za ta sarrafa tsarin jagorantar shi yadda take so. Yanki ne mai tarihi, da cibiyoyi, da yake da burikan shi. Kasashen da suka sha wahalar juyin mulki da danniyar Amurka a karni na 20, tarihin Guatemala 1954, da Chile 1973, Nicaragua a 1980, da Panama 1989, yanzu shi zai haskaka musu hanyar ganin wannan sabon harin da aka kai wa Caracas a shekarar 2026.

Duk wani shiri da Amurka za ta aiwatar, babu abin da zai haifar, face maimaita tarihin abin da ta taba yi a yankin. Don haka, ba laifi ba ne, in an ce, Amurka ba ta ganin yankin a matsayin makwabciya sai dai kawai kamar wani yankin bayinta ko kuma filin gwada karfin sojinta.

 

 

 

Amurka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Anguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

Hadin Tsawon Gashi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Anguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Anguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.