ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron G20 Ya Nuna Makomar Duniya Mai Haske

by Sulaiman
7 months ago
G20

A jiya Asabar aka kaddamar da taron kolin kungiyar G20 a Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu, tare da zartas da wata hadaddiyar sanarwa.

Kafin hakan, kasar Amurka ta ki tura babban jami’i zuwa taron, bisa dalilin wai gwamnatin kasar Afirka ta Kudu tana “cin zarafin ‘yan kasar fararen fata”, kana ta yi gargadin cewa, kada a zartas da wata sanarwa a wajen taron, a matsayin ra’ayi daya da mambobin kungiyar G20 suka cimma. Sai dai abun da ya faru daga bisani ya nuna cewa, umarnin da kasar Amurka ta bayar ba shi da amfani, in ban da janyo wa kanta wulakanci.

Wannan lamarin ya zama wata nasara da kasar Afirka ta Kudu ta samu, kuma ta nuna karfafar matsayin ra’ayin kasancewar mabambantan bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya. Kamar yadda kakakin shugaban kasar Afirka ta Kudun Vincent Magwenya ya fada, cewa zartas da wannan hadaddiyar sanarwa a wajen taron ya nuna yadda kasashe daban daban suke kokarin hadin gwiwa da juna, da goyon bayan ra’ayin kasancewar mabambantan bangarori masu fada-a-ji a duniya. Hakan ya kuma dace da babban taken taron G20 na wannan karo, wato “Hadin Kai, da Daidaito da kuma Dorewa.”

ADVERTISEMENT

A nata bangare, kasar Sin ita ma ta jaddada matsayinta, na rungumar ra’ayin kasancewar mabambantan bangarori masu fada-a-ji a duniya, a wajen taron, inda firaministan kasar Sin Li Qiang, ya yi kira da a gaggauta yin gyaran fuska ga kungiyoyin kasa da kasa, da kara fitowa da muryar kasashe masu tasowa a duniya, da kafa wani budadden tsarin tattalin arziki da ciniki mafi adalci.

Hakika kasar Sin ta dade tana kokarin daukaka matsayin tunanin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, inda abubuwan da kasar ta yi suka hada da, ba da taimako ga kungiyar kasashen Afirka ta AU don ta zama mambar kungiyar G20, da habaka tsare-tsaren kungiyoyin BRICS, da SCO da dai sauransu. Ban da haka, kungiyar shiga tsakani don daidaita sabani ko (IOMed) da kasar Sin da sauran kasashe fiye da 30 suka kafa, ta samar da wata sabuwar hanyar daidaita rikici, wadda ba ta cikin tsare-tsaren neman kwantar da rikici da kasashen yamma suka tsara.

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Sai dai wani abun tambayar shi ne ko mene ne dalilin da ya sa kasar Sin take goyon bayan ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya? Amsar ita ce hakan ya dace da tunanin da kasar ke kokarin yayatawa, na kafa “Al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya”. Yayin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci tarukan kungiyar G20 a lokacin baya, ya taba bayyana tunanin kamar haka, “Ci gaba na bai daya na kasashe daban daban shi ne ci gaba na gaske”. Kana ya ce ya kamata a sanya ci gaban tattalin arzikin duniya ya amfani kasashe daban daban, inda za a yi kokarin tabbatar da adalci da daidaito, maimakon barin wata kasa a baya.

Kafofin yada labarai na kasashen yamma, suna son bayyana takarar da kasashen Amurka da Sin suke yi a matsayin abu mai matukar muhimmanci dake faruwa a duniya. Sai dai idan an kwatanta tunanin da kasar Sin da sauran kasashe suke goyon bayansa, da matakan radin kai da wasu kasashe ke dauka, za mu iya ganin cewa, babban sabani mafiya tasiri a duniya, shi ne bambancin ra’ayin da ake samu tsakanin kasashe masu tasowa, da kasashe masu sukuni dake yammacin duniya, inda wani bangarensu ke rungumar ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, yayin da dayan bangare ke neman kiyaye tsohon tsari na “Kasashen yamma ke ba da umarni, don sauran kasashe su bi shi”.

Sai dai tabbas, sabon tsari zai maye gurbin tsohon, ganin yadda shugabannin kasashe daban daban suka rike hannuwan juna a wajen taron kolin kungiyar G20 da ya gudana a nahiyar Afirka a wannan karo, kana gargadin da kasar Amurka ta bayar, bai hana su cimma matsaya daya ta daukaka ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya ba. Da haka, ma iya cewa taron na wannan karo ya kara tabbatar mana da makomar duniya mai haske. (Bello Wang)

 

G20
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
Next Post
Ƴan Ta’adda Sun Sace Mata Manoma 13 A Borno

Ƴan Ta’adda Sun Sace Mata Manoma 13 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.