Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa, zai goyi bayan duk wanda ya fito a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na haɗakar jam’iyyun adawa a ƙarƙashin jam’iyyar ADC gabanin zaɓen shekarar 2027, yana mai jaddada cewa haɗin kai tsakanin ‘ya’yan Jam’iyyar yana da matuƙar muhimmanci wajen kare dimokuraɗiyyar Nijeriya.
Da yake magana a wata hira da ‘ARISE News Channel’ a yammacin ranar Laraba, Atiku ya yi watsi da ra’ayin cewa, fafatawar neman tikitin haɗakar za ta ta’allaka ne kan zartar da ‘yan takara, yana mai cewa tsarin zai fi mayar da hankali kan cimma matsaya guda tsakanin masu ruwa da tsaki.
Da aka tambaye shi ko zai iya janyewa daga takarar, Atiku ya ce: “Ba batun janyewa ba ne, amma shin zan goyi bayan haɗakarmu? Mataki na farko shi ne mu nemi matsaya guda. Idan hakan bai yiwu ba, sai mu koma tsarin zaɓe. Tabbas, zan goyi bayan duk wanda ya fito,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa: “Za mu yi ƙoƙarin cimma matsaya guda. Idan hakan ba ta mu samu ba, sai mu je tsarin zaɓe.”















Discussion about this post