ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tilas A Nuna Adawa Da Hada Hannu Tsakanin Amurka Da Taiwan

by CMG Hausa
3 years ago
Protesters opposed to Taiwanese independence gather at a hotel where Taiwanese President Tsai Ing-wen is expected to arrive in New York, Wednesday, March 29, 2023. (AP Photo/Seth Wenig)

Protesters opposed to Taiwanese independence gather at a hotel where Taiwanese President Tsai Ing-wen is expected to arrive in New York, Wednesday, March 29, 2023. (AP Photo/Seth Wenig)

Yau Alhamis ne jagorar mahukuntan yankin Taiwan na kasar Sin Tsai Ing-wen, ta gana da kakakin majalisar wakilan kasar Amurka Kevin McCarthy, yayin da Amurka ta baiwa jami’ar damar bi ta cikin Amurka, a hanyarta ta yin wani bulaguro. 

Wannan ne karo na 2 da Amurka da Taiwan suka hada hannu wajen daukar matakan takala ta fuskar siyasa, bayan Nancy Pelosi ta ziyarci Taiwan a bara. Abin da Amurka ta yi ya saba wa ka’idar kasar Sin daya tak a duniya, da sanarwoyi 3 wadanda Sin da Amurka suka amince da su bisa hadin gwiwa, ya kuma illata ikon mulkin kasar Sin, da cikakkun yankunan kasar Sin, ya kuma sake aikewa wa ‘yan a-ware masu neman ‘yancin Taiwan munanan sakonni.

  • Sin: Fannin Sayayya Da Na Yawon Shakatawa Na Kara Farfadowa A Rubu’in Farko Na Bana

A hannu guda kuma, kasashen duniya sun kara gane cewa, mahukuntan Taiwan karkashin shugabancin DPP, suna kara yunkurin hada hannu da Amurka, yayin da wasu Amurkawa suke neman amfani da Taiwan wajen sarrafa akalar Sin, lamarin da ya kasance ainihin dalilin da ya sa ake rura wuta tsakanin gabobi 2 na mashigin tekun Taiwan.

ADVERTISEMENT

Batun Taiwan, babbar moriyar kasar Sin ce mai matukar muhimmanci, kuma tushe ne na huldar da ke tsakannin Sin da Amurka ta fuskar siyasa, kana kuma shi ne jan-layi na farko da ba zai yiwu a tsallaka shi ba, a dangantakar Sin da Amurka. Kaza lika matakan da Amurka ta dauka, da kuma kalamanta, sun sake saba wa alkawarin da ta yi na bin ka’idar kasar Sin daya tak a duniya. Amurka tana ta daukar matakan takala.

Taiwan, yanki ne na kasar Sin. Al’ummar kasar Sin ne kadai suke da ikon daidaita batun na Taiwan. Makarkashiyar da Amurka da Taiwan suke kullawa, ba za ta sauya tarihin Taiwan na kasancewar bangaren kasar Sin ba, ba za ta murde gaskiya ba, ba za ta hana dinkuwar kasar Sin baki daya ba, ba za ta hana yawancin kasashen duniya su amince, da kuma goyon bayan ka’idar kasar Sin daya tak a duniya ba.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Tun tuni kasar Sin ta bayyana kin yarda da hada hannu tsakanin Amurka da Taiwan, kuma za ta mayar da martani. Babu wanda ya isa ya raina kudiri, da karfin da Sinawa suke da shi na kare ikon mallakar kasa da cikakkun yankunanta. (Tasallah Yuan)

 

 

Taiwan
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Bankin Duniya Ya Bai Wa Nijeriya Tallafin Dala Miliyan 800

Bankin Duniya Ya Bai Wa Nijeriya Tallafin Dala Miliyan 800

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.