Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya sanya hannu kan Dokar Zaɓe ta 2022 (wadda aka yi wa kwaskwarima) domin fara aiki a 2026.
Wannan ya biyo bayan amincewar Majalisar Dokoki bayan watanni na tattaunawa.
- Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Jam’iyyar APC A Kano
- Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Sabuwar Shekara Ga Abokai A Jihar Iowa Ta Amurka
Dokar ta jawo muhawara mai zafi, musamman kan yadda za a tura sakamakon zaɓe.
Wasu ‘yan majalisa da ‘yan adawa sun ce a tura sakamako ta lantarki a lokacin da ake gudanar da zaɓe domin fayyace gaskiya, yayin da wasu suka nuna damuwa kan matsalolin sadarwa da kuma amfani da takardu.
A Majalisar Dattijai, rashin jituwa kan Tanadi na 60 da ke magana kan tura sakamako na lantarki ya haifar da rarrabuwar kawuna.
Daga cikin ‘yan Majalisa 70, 55 sun goyi bayan ci gaba da amfani da takardu idan amfani da lantarki ya gaza, yayin da 15 suka ƙi amincewa.
Haka kuma, Majalisar Wakilai ta nuna rashin jituwa lokacin da aka ƙalubalanci ƙudirin cire dokar, amma Shugaban Majalisar ya tabbatar da dokar.
Sabuwar dokar ta zo ne kafin zaɓen 2027, wanda ya haɗa da zaɓen shugaban ƙasa, Majalisar Tarayya, gwamnonin jihohi da majalisun jihohi.















Discussion about this post