Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi murabus, kan cewar gwamnatinsa ta gaza magance matsalolin tattalin arziƙi da tsaro da ke addabar Nijeriya.
A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya ce dole ne shugabanni su kasance masu ɗaukar alhakin ayyukansu.
Ya yi kafa misali murabus ɗin Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, a matsayin aya kan jagoranci.
Obi ya ce matuƙar Tinubu ba zai iya kare rayukan jama’a ba ya kamata ya sauka daga mulki.
Ya kuma tunatar da jama’a alƙawuran da Tinubu ya yi a lokacin yaƙin neman zaɓe kan inganta wutar lantarki, yaƙi da cin hanci da rashawa, da kyautata rayuwar ‘yan Nijeriya.
A cewarsa, tun bayan hawan Tinubu mulki, matsalolin tattalin arziƙi, rashin isasshiyar wutar lantarki da rashin tsaro suka ƙara ƙamari.
Obi ya ce waɗannan matsaloli sun nuna gazawa wajen shugabanci, don haka ya buƙaci shugaban ƙasa ya yi murabus domin ƙarfafa al’adar ɗaukar alhaki da inganta dimokuraɗiyya a Nijeriya.















Discussion about this post