Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yaba wa jami’an soji da sauran jami’an tsaro, inda ya bayyana cewa; kasar na sane da irin gudunmawar da suke bayarwa, don kawo karshen ta’addanci da ‘yan ta’adda.
Shugaban, a wani sako da ya wallafa a shafinsa na D, ya kuma yi jawabi ga jami’an soji da sauran jami’an tsaro, inda ya yaba wa sojojin bisa sadaukarwar da suke yi, inda ya kwatanta su a matsayin garkuwar kare ‘yan Nijeriya da kuma tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar.
Yayin da yake bayyana yaki da rashin tsaro a matsayin aikin da sojoji suka sanya a gaba, shugaban kasar ya ce; aiki ne na kasa, inda ya bukaci ‘yan kasar da su tallafa wa jami’an tsaro “ta hanyar samar da bayanai masu amfani a kan lokaci, da zarar ka ga wani abu, sai ka yi maza ka sanar, haka nan idan ka san wani abu, sai ka yi gaggawar kai rahoto,” in ji shi.
Haka zalika, ya rubuta cewa; “Ina yaba wa dukkan sojojinmu da ke sahun gaba kan kishin kasa, wajen yaki da ta’addanci ta kowane fanni. Babau shakka, kun tsaya a matsayin garkuwa tsakanin ‘yan kasa, wadanda ba su ji ba, ba su gani ba, domin kawar da masu neman hana zaman lafiya, tsaro da martabar al’ummarmu.”
Kazalika, ya yaba wa sojojin da suka dauki nauyin kare ‘yan Nijeriya a wuraren da babu zaman lafiya, yana mai cewa; kasar ba za ta dauki wannan sadaukarwa da wasa ba ko kadan.
“Wannan yakin, ba mai sauki ba ko kadan, domin kuwa ya zo da abubuwa na rashin jin dadi, matsi da kuma sadaukarwa, amma, kun tsaya tsayin daka wajen kokarin magance shi. Ana sane tare da amincewa da hidimarku da kuma sadaukarwar da kuka yi, wannan wannan kasa taku ba za ta taba dauka da wasa ba.”
“Ga duk wani jami’in soja, ‘yansanda, DSS, Cibil Defence, jami’an leken asiri, jami’an tsaro na cikin gida da duk wanda ke aiki dare da rana don tabbatar da tsaron Nijeriya, ina mai yi muku godiya, na gode kwarai da gaske.
“Ina kuma jinjina wa iyalan wadannan jami’ai na tsaro, wadanda yawa daga cikinku, wadannan jami’ai sun yi nisa da ku a dare da rana, don haka Nijeriya na sane da wannan sadaukarwa taku.
“Muna girmama wadanda suka biya mafi girman farashi don kare kasarmu. Sunayensu ba za su yi ta yawo a cikin al’umma ba, amma karfinsu da ayyukansu na ceton al’ummomi a kullum yana yawo a tsakanin al’ummar.”
Shugaban ya jaddada muhimmancin aikin soja, yana mai jaddada cewa; yaki da ta’addanci ba aikin soji ne kadai ba.
“Hakkin kasa ne, ‘yan kasa su tallafa wa jami’an tsaronmu ta hanyar samar da bayanai masu amfani a kan lokaci, idan ka ga wani abu sai ka sanar cikin gaggawa, ta hanyar bayar da rahoto.
“Nijeriya ba za ta mika wuya don tsoro ba, ba za mu bari ‘yan ta’adda da ‘yan fashi masu garkuwa da mutane ko masu tsattsauran ra’ayi su bayyana wa duniya wace al’umma ce mu ba, domin kuwa tashin hankalin ba shi ne asalinmu ba.
“Saboda haka, ga sojojinmu da duk sauran masu kishin kasa, na gode da jajircewarku matuka,” kamar yadda ya rubuta.















Discussion about this post