ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Goyon Bayan Gwamna Lawal Ga Sojoji Ba Kasafai Ake Samun Irin Sa Ba — Babban Hafsan Tsaro

by Sulaiman
2 months ago

Babban Hafsan Tsaron Nijeriya, Janar Olufemi Oluyede, ya yaba da irin gagarumin goyon bayan da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ke bai wa rundunar Operation Fansan Yamma, yana mai cewa irin wannan tallafi ba kasafai ake ganin irinsa ba.

Janar Oluyede ya bayyana hakan ne a yayin wata ziyarar aiki da ya kai Jihar Zamfara, inda ya gana da gwamnan tare da duba hedikwatar rundunar Operation Fansan Yamma da ke Gusau.

A lokacin ziyarar girmamawa da ya kai Gidan Gwamnatin Jihar Zamfara, Babban Hafsan Tsaron ya jaddada muhimmancin haɗin kai tsakanin gwamnatin jiha da rundunar sojoji wajen magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin.

ADVERTISEMENT

Ya ce, ya zo jihar ne domin nuna godiya ga gwamnan bisa irin rawar da yake takawa wajen tallafa wa rundunar, yana mai ƙarawa da cewa haɗin kai tsakanin gwamnati da al’umma na da matuƙar muhimmanci wajen shawo kan ƙalubalen tsaro.

Janar Oluyede ya kuma yaba wa al’ummar jihar bisa yadda suke karbar jami’an tsaro hannu bibbiyu, yana mai jaddada cewa Nijeriya ƙasa ɗaya ce da ke buƙatar haɗin kan kowa domin fuskantar barazanar tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Ya ƙara da cewa, ya ziyarci hedikwatar rundunar Operation Fansan Yamma, inda ya gana da jami’an tsaro, ya saurari ƙalubalen da suke fuskanta, tare da warware wasu daga cikinsu, yayin da sauran aka ɗauki matakan da suka dace domin magance su nan gaba.

A nasa bangaren, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa magance matsalar ‘yan bindiga a Zamfara na nufin an rage kusan kashi 75 cikin 100 na matsalar a duk faɗin Nijeriya.

Ya ce, wajibi ne shugabanni su ɗauki matakan da suka dace domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a, yana mai jaddada cewa babu wani ƙarfi da ya wuce na rundunar sojojin Nijeriya.

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatin sa na ci gaba da bayar da cikakken goyon baya ga jami’an tsaro, yana mai tunatar da cewa a kwanan nan Ministan Tsaro ya ƙaddamar da sabbin motocin aiki na zamani da gwamnatin jihar ta samar domin taimaka wa rundunar.

Ya kuma jaddada cewa duk wani ci gaba ba shi da amfani idan babu tsaro, don haka ne gwamnatin jihar ke bai wa bangaren tsaro fifiko a cikin manufofinta.

Gwamna Lawal ya gode wa Shugaban Ƙasa bisa tallafin da yake bai wa jihar, tare da jaddada buƙatar ƙarin goyon baya domin cimma nasarar yaƙi da matsalar tsaro.

A ƙarshe, ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki kafaɗa da kafɗa da rundunar sojoji da sauran hukumomin tsaro domin kawo ƙarshen matsalar ’yan bindiga a jihar.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki
  • Sulaiman
    Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

MASU ALAKA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
Labarai

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya
Manyan Labarai

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Next Post
Kamfanonin Jamus Na Fatan Kara Amfani Da Damammaki A Kasuwar Sin

Kamfanonin Jamus Na Fatan Kara Amfani Da Damammaki A Kasuwar Sin

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.