Tun daga kafuwar jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin kawo yanzu, daya daga manyan kudurorinta shi ne tabbatar da walwalar daukacin al’ummun kasar. Wato dai tabbatar da cewa ba a bar kowa a baya ba, da ci gaba da zamanantar da kasa. A bangaren alaka da sauran kasashen waje ma, burin zamanantarwa daya ne daga kudurorin ci gaba da Sin ke mayar da hankali a kai.
Domin taimakawa karin kasashe masu tasowa su cimma nasarar bunkasa kansu bisa turbar zamanantarwa gwargwadon yanayin da suke ciki, kasar Sin na yin matukar kokari, ta yadda hakan ke haifar da sakamako na cimma moriyar bai daya.
A wannan lokaci, kasar Sin ta shiga gaba wajen jagorantar hakan, musamman a wasu muhimman fannoni, wadanda suka hada da bunkasa cin gajiyar makamashi mai tsafta, da inganta harkar noma, da samar da ababen more rayuwa da sauransu. Muna ma iya cewa, kasar Sin ta zama “Zakaran gwajin dafi” a fannin ingiza ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba tsakanin kasashen duniya.
Ko shakka babu, salon kasar Sin na zamamantarwa zai amfani kaso mai yawa na kasashen duniya baya ga su kansu Sinawa, kuma tuni aka fara ganin sakamakonsa a sassa daban daban na kasar.
A wasu sassan yammacin duniya, salon zamanantarwa ya fi karkata ga tattalin arziki, da samar da ababen more rayuwa na zamani, amma a bangaren Sin, zamanantarwa na kunshe da karin alfanu, ciki har da zamanantar da hukumomi, da ilimi da tsarin siyasa.
A mahangar kasar Sin, ba za a iya cimma cikakkiyar nasara ba muddin ba a zamanantar da hukumomi, da ilimi da tsarin jagoranci ba.Yayin da turbar ci gaban kasar Sin ke kara zurfafa, daga saurin bunkasa tattalin arziki zuwa tattalin arziki na manyan fasahohi, a daya bangaren salon kasar na zamanantarwa na kara zama kyakkyawan misali, abun koyi ga sauran kasashe masu tasowa.
Salon kasar Sin na zamanantarwa na taimakawa kasar ita kanta, da tushen samun ci gaba da walwalar al’umma, ya kuma zamo kashin bayan gina managarcin tsarin jagoranci mai sanya al’umma gaban komai. (Saminu Alhassan)














