HausaWakilin musamman na shugaba Xi Jinping na kasar Sin, wato Shao Hong, zai halarci bikin rantsuwar kama aiki ta shugaban kasar Congo (Brazzaville) Denis Sassou-N’Guesso a ranar Alhamis 16 ga watan nan, bikin da za a gudanar a birnin Brazzaville.
A cewar kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Shao wanda kuma shi ne mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar bayar da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin ko CPPCC, zai halarci bikin rantsuwar ne bisa gayyatar da shugaba Sassou-N’Guesso ya yi masa. (Saminu Alhassan)
ADVERTISEMENT














Discussion about this post