Mai riƙe da muƙamin Minority Whip a Majalisar Wakilai, Hon. Ali Isa JC, ya yi murabus daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), yana mai danganta hakan da rikicin cikin gida da kuma abin da ya kira rashin bin ƙa’idar dimokuraɗiyya a cikin jam’iyyar.
A cikin wasiƙar murabus ɗinsa mai ɗauke da kwanan watan 14 ga Afrilu, 2026, wadda aka aika wa shugaban mazabar Kindiyo da ke ƙaramar hukumar Balanga a Jihar Gombe, Isa JC ya ce matakin nasa ya fara aiki nan take.
Dan majalisar, wanda ke wakiltar mazaɓar Balanga/Billiri a Majalisar Tarayya, ya bayyana cewa ficewarsa ta samo asali ne daga damuwa kan yadda ake tafiyar da jam’iyyar, yana mai zargin cewa wasu ƙarfi sun kwace iko da tafiyar da ita ta hanyar da ta saɓa da manufofinta na asali.
Ya ce: “An tilasta min ɗaukar wannan mataki ne sakamakon yadda wasu ƙungiyoyi marasa bin ƙa’idar dimokuraɗiyya suka ƙwace jam’iyyar domin manufofi da suka saɓa da ginshiƙanta, lamarin da ya haifar da shugabanci mai ɓangarori.”
Isa JC ya ƙara da cewa ya yanke wannan shawara ne bayan tattaunawa mai zurfi da iyalansa, abokan siyasa, da sauran masu ruwa da tsaki.
“Bayan tattaunawa mai zurfi da iyalaina, abokan siyasa, da sauran masu ruwa da tsaki, na fahimci cewa makomata ta siyasa, da kuma ta al’ummar da suka ba ni amanar wakilci, ba ta cikin PDP,” in ji shi.
Ya jaddada cewa fifikonsa shi ne jin daɗin al’ummar mazaɓarsa da kuma ci gaban siyasarsu, yana mai cewa akwai buƙatar samun wani dandali mafi dacewa domin kare muradunsu.
“Na yi imanin cewa al’ummar mazaɓata sun cancanci wani dandali da zai fi kare muradunsu da makomarsu ta siyasa,” ya ƙara da cewa.
Duk da ficewarsa, Isa JC ya gode wa jam’iyyar PDP bisa damar da ta ba shi na wakiltar al’ummarsa a Majalisar Tarayya.
“Ina miƙa godiyata ga shugabanni da mambobin jam’iyyar da suka ba ni dama ta wakiltar al’ummar Balanga/Billiri. Zan ci gaba da kasancewa mai godiya a gare ku, ina kuma yi muku fatan alheri,” in ji shi.
Ficewar tasa na ƙara jaddada damuwar da ake da ita kan rikice-rikicen cikin gida a jam’iyyar PDP, yayin da ake ci gaba da sauye-sauyen siyasa gabanin zaɓen shekarar 2027.















Discussion about this post