ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Majalisar Wakilai, Ali Isa JC, Ya Fice Daga PDP

by Muhammad
2 months ago

Mai riƙe da muƙamin Minority Whip a Majalisar Wakilai, Hon. Ali Isa JC, ya yi murabus daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), yana mai danganta hakan da rikicin cikin gida da kuma abin da ya kira rashin bin ƙa’idar dimokuraɗiyya a cikin jam’iyyar.

A cikin wasiƙar murabus ɗinsa mai ɗauke da kwanan watan 14 ga Afrilu, 2026, wadda aka aika wa shugaban mazabar Kindiyo da ke ƙaramar hukumar Balanga a Jihar Gombe, Isa JC ya ce matakin nasa ya fara aiki nan take.

Dan majalisar, wanda ke wakiltar mazaɓar Balanga/Billiri a Majalisar Tarayya, ya bayyana cewa ficewarsa ta samo asali ne daga damuwa kan yadda ake tafiyar da jam’iyyar, yana mai zargin cewa wasu ƙarfi sun kwace iko da tafiyar da ita ta hanyar da ta saɓa da manufofinta na asali.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “An tilasta min ɗaukar wannan mataki ne sakamakon yadda wasu ƙungiyoyi marasa bin ƙa’idar dimokuraɗiyya suka ƙwace jam’iyyar domin manufofi da suka saɓa da ginshiƙanta, lamarin da ya haifar da shugabanci mai ɓangarori.”

Isa JC ya ƙara da cewa ya yanke wannan shawara ne bayan tattaunawa mai zurfi da iyalansa, abokan siyasa, da sauran masu ruwa da tsaki.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Bayan tattaunawa mai zurfi da iyalaina, abokan siyasa, da sauran masu ruwa da tsaki, na fahimci cewa makomata ta siyasa, da kuma ta al’ummar da suka ba ni amanar wakilci, ba ta cikin PDP,” in ji shi.

Ya jaddada cewa fifikonsa shi ne jin daɗin al’ummar mazaɓarsa da kuma ci gaban siyasarsu, yana mai cewa akwai buƙatar samun wani dandali mafi dacewa domin kare muradunsu.

“Na yi imanin cewa al’ummar mazaɓata sun cancanci wani dandali da zai fi kare muradunsu da makomarsu ta siyasa,” ya ƙara da cewa.

Duk da ficewarsa, Isa JC ya gode wa jam’iyyar PDP bisa damar da ta ba shi na wakiltar al’ummarsa a Majalisar Tarayya.

“Ina miƙa godiyata ga shugabanni da mambobin jam’iyyar da suka ba ni dama ta wakiltar al’ummar Balanga/Billiri. Zan ci gaba da kasancewa mai godiya a gare ku, ina kuma yi muku fatan alheri,” in ji shi.

Ficewar tasa na ƙara jaddada damuwar da ake da ita kan rikice-rikicen cikin gida a jam’iyyar PDP, yayin da ake ci gaba da sauye-sauyen siyasa gabanin zaɓen shekarar 2027.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sin Ta Harba Rokar Lijian-1 Y12 Dauke Da Taurarin Dan Adam Takwas

Sin Ta Harba Rokar Lijian-1 Y12 Dauke Da Taurarin Dan Adam Takwas

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.