ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Majalisar Wakilai, Ali Isa JC, Ya Fice Daga PDP

by Muhammad
3 months ago

Mai riƙe da muƙamin Minority Whip a Majalisar Wakilai, Hon. Ali Isa JC, ya yi murabus daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), yana mai danganta hakan da rikicin cikin gida da kuma abin da ya kira rashin bin ƙa’idar dimokuraɗiyya a cikin jam’iyyar.

A cikin wasiƙar murabus ɗinsa mai ɗauke da kwanan watan 14 ga Afrilu, 2026, wadda aka aika wa shugaban mazabar Kindiyo da ke ƙaramar hukumar Balanga a Jihar Gombe, Isa JC ya ce matakin nasa ya fara aiki nan take.

Dan majalisar, wanda ke wakiltar mazaɓar Balanga/Billiri a Majalisar Tarayya, ya bayyana cewa ficewarsa ta samo asali ne daga damuwa kan yadda ake tafiyar da jam’iyyar, yana mai zargin cewa wasu ƙarfi sun kwace iko da tafiyar da ita ta hanyar da ta saɓa da manufofinta na asali.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “An tilasta min ɗaukar wannan mataki ne sakamakon yadda wasu ƙungiyoyi marasa bin ƙa’idar dimokuraɗiyya suka ƙwace jam’iyyar domin manufofi da suka saɓa da ginshiƙanta, lamarin da ya haifar da shugabanci mai ɓangarori.”

Isa JC ya ƙara da cewa ya yanke wannan shawara ne bayan tattaunawa mai zurfi da iyalansa, abokan siyasa, da sauran masu ruwa da tsaki.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

“Bayan tattaunawa mai zurfi da iyalaina, abokan siyasa, da sauran masu ruwa da tsaki, na fahimci cewa makomata ta siyasa, da kuma ta al’ummar da suka ba ni amanar wakilci, ba ta cikin PDP,” in ji shi.

Ya jaddada cewa fifikonsa shi ne jin daɗin al’ummar mazaɓarsa da kuma ci gaban siyasarsu, yana mai cewa akwai buƙatar samun wani dandali mafi dacewa domin kare muradunsu.

“Na yi imanin cewa al’ummar mazaɓata sun cancanci wani dandali da zai fi kare muradunsu da makomarsu ta siyasa,” ya ƙara da cewa.

Duk da ficewarsa, Isa JC ya gode wa jam’iyyar PDP bisa damar da ta ba shi na wakiltar al’ummarsa a Majalisar Tarayya.

“Ina miƙa godiyata ga shugabanni da mambobin jam’iyyar da suka ba ni dama ta wakiltar al’ummar Balanga/Billiri. Zan ci gaba da kasancewa mai godiya a gare ku, ina kuma yi muku fatan alheri,” in ji shi.

Ficewar tasa na ƙara jaddada damuwar da ake da ita kan rikice-rikicen cikin gida a jam’iyyar PDP, yayin da ake ci gaba da sauye-sauyen siyasa gabanin zaɓen shekarar 2027.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya
Labarai

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Next Post
Sin Ta Harba Rokar Lijian-1 Y12 Dauke Da Taurarin Dan Adam Takwas

Sin Ta Harba Rokar Lijian-1 Y12 Dauke Da Taurarin Dan Adam Takwas

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.