Tsakanin ranakun Alhamis zuwa jiya Juma’a, an gudanar da taron mataimakan ministoci ko wakilan musamman, na kasashe membobin kungiyar BRICS dangane da batutuwan yankin Gabas ta Tsakiya.
Taron ya gudana ne a birnin New Delhi na kasar India. Kuma wakilin musamman na gwamnatin kasar game da Gabas ta Tsakiya Zhai Jun, ya jagoranci tawagar kasar Sin zuwa taron.
Da yake tsokaci yayin taron, Zhai Jun ya ce ana cikin wani yanayi mai tsanani a Gabas ta Tsakiya, kuma tushen tsagaita wuta da aka cimma yana da matukar rauni.
Ya ce a baya kadan, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarwarin karewa, da inganta zaman lafiya da daidaito a Gabas ta Tsakiya, da gabatar da basirar kasar Sin game da kwantar da wutar yaki a shiyyar, da warware rikicin da ake ciki yanzu haka.
Don haka a cewarsa, kamata ya yi kasashe membobin BRICS su nacewa matakai masu zaman kansu, da dogaro da ikonsu, wajen wanzar da adalci da da’a, kana su kara ingiza karsashi, da daidaito, da kuzari ga aikin wanzar da zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya da duniya baki daya.
Yayin zaman, dukkanin sassa mahalarta sun zurfafa musayar fahimta game da batutuwa masu jan hankali a Gabas ta Tsakiya, sun kuma nuna damuwa game da yanayin dar-dar da ake ciki a shiyyar.
Kana sun jaddada yadda suke mutunta ikon mulkin kai, da ‘yanci, da martabar yankunan dukkanin kasashen yankin, kana sun yi kira da a warware dukkanin sabani ta hanyoyin siyasa da diflomasiyya. (Mai fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post