Jam’iyyar NNPP ta bayyana cewa za ta ci gaba da gudanar da tarurrukanta na jam’iyya, duk da rikicin da ke tattare da bin umarnin kotu da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC).
Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da wanda ya kafa jam’iyyar, Boniface Aniebonam, ya fitar a ranar Asabar a Lagos.
Aniebonam ya ce jam’iyyar ta riga ta miƙa jadawalin shirinta na gudanar da tarukan jam’iyya, zaɓen fidda gwani da babban taron ƙasa ga INEC, kuma za ta shiga dukkan zaɓuɓɓuka, ciki har da na shugaban ƙasa a 2027.
Ya zargi INEC da jinkirta saka sunayen shugabannin kwamitin gudanarwa na ƙasa (NWC) na jam’iyyar da Dr Agbo Major ke jagoranta, duk da umarnin kotu.
A cewarsa: “Jinkirin da INEC ke yi wajen bin umarnin kotu, da kuma rikicin shugabanci da ya daɗe yana gudana a kotu, sun hana NNPP da mambobinta damar shiga wasu zaɓuɓɓuka a faɗin ƙasa.”
Ya ƙara da cewa saboda haka ne suka yanke shawarar ci gaba da gudanar da tarukan jam’iyya da babban taron ƙasa, yayin da suke jiran INEC ta bi umarnin kotu.
“Ba za mu ci gaba da hana mambobinmu damar shiga zaɓe a Nijeriya ba. Zaɓen 2027 babban zaɓe ne, kuma lokaci na tafiya, dole ne mu shirya tun da wuri,” in ji shi.
Aniebonam ya jaddada cewa jam’iyyar ba za ta daina fafutukar ganin INEC ta sabunta bayananta tare da amincewa da shugabancin Dr Agbo Major ba.
Ya ce sun yi tsammanin INEC za ta bi umarnin kotu, amma hakan bai faru ba, lamarin da ya sa suka nemi tattaunawa da hukumar domin fahimtar dalilin rashin bin umarnin kotu.
Ya kuma jaddada cewa umarnin kotu ya fi ƙarfin duk wani mataki ko hukunci da INEC za ta ɗauka, har ma da matakan ladabtarwa na cikin gida na jam’iyya.
A ƙarshe, ya kawo misalai na baya da suka nuna yadda rashin bin umarnin kotu ya taɓa haifar da matsaloli a harkokin zaɓe a Nijeriya.















Discussion about this post