Majalisar Dinkin Duniya ta gudanar da tattaunawar gwamnatoci kan batun “Raba kujeru cikin adalci da kara yawan membobin Kwamitin Sulhu” da sauran batutuwan da suka shafi Kwamitin Sulhu a jiya Juma’a. Wakilin dindindin na kasar Sin dake MDD Fu Cong ya jaddada a karshen jawabinsa cewa, Japan ta ki yin waiwaye a kan ta’asar mamayar da ta yi a tarihi, kuma ta keta tsarin kasa da kasa bayan yakin duniya na II, tare da tsoma baki cikin harkokin da suka shafi mulkin kai na sauran kasashe, matakan da suka kawo sabuwar barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali na shiyyar. Irin wannan kasa ba ta cancanci zama mamba na dindindin a kwamitin sulhu ba.
Yayin da yake ambaton batun yin kwaskwarima ga kwamitin sulhun, wakilin ya jaddada ra’ayoyinsa guda uku, da farko, bai kamata kwamitin sulhu ya zama “kulob” na manyan kasashe da kasashe masu arziki ba, kuma ba za a iya barin gyara ya amfani wasu kalilan kasashe kawai ba. Na biyu, kamata ya yi a kara wakilci da ikon fada-a-ji na kasashe masu tasowa a harkokin duniya, da kara samar da dama ga matsakaita da kanana kasashe masu cin gashin kansu a manufofin harkokin waje su shiga cikin kwamitin sulhu, musamman ma a gyara rashin adalci a tarihi da Afirka ta fuskanta, kuma a ba da fifiko na musamman wajen biyan bukatun Afirka. Na uku, ba wai kawai za a yi la’akari da yanayin duniya na yanzu ba, a’a, ya kamata a rika tsara gyare-gyaren tare da hangen nesa bisa manyan tsare-tsare da kuma dogon zango. (Mai fassara Bilkisu Xin)















Discussion about this post